ترجمة معاني القرآن الكريم - الترجمة الهوساوية - أبو بكر جومي * - فهرس التراجم

XML CSV Excel API
تنزيل الملفات يتضمن الموافقة على هذه الشروط والسياسات

ترجمة معاني سورة: البلد   آية:

سورة البلد - Suratu Al'balad

لَآ أُقۡسِمُ بِهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ
Bã sai Na yi rantsuwa da wannan gari* ba.
* Allah Ya ce ba sai Ya yi rantsuwa da Makka ba, sa'an nan zã a san darajarta a lõkacinda Annabi yake a cikinta, kuma shi yana da haƙƙin zama a cikinta mahaifansa da zurriyarsa duka, ko da yake zai yi hijira sabõda fitinar kãfirai mãsu halaka dũkiyarsu kan adãwa da shi. Dã sun yi amfãni da dukiyar ga ayyukan alheri, dã yã fi musu.
التفاسير العربية:
وَأَنتَ حِلُّۢ بِهَٰذَا ٱلۡبَلَدِ
Alhãli kai kanã mai sauka a cikin wannan gari.
التفاسير العربية:
وَوَالِدٖ وَمَا وَلَدَ
Da mahaifi da abin da ya haifa.
التفاسير العربية:
لَقَدۡ خَلَقۡنَا ٱلۡإِنسَٰنَ فِي كَبَدٍ
Lalle ne, Mun halitta mutum cikin wahala.
التفاسير العربية:
أَيَحۡسَبُ أَن لَّن يَقۡدِرَ عَلَيۡهِ أَحَدٞ
Kõ yanã zaton bãbu wani mai iya sãmun iko, a kansa?
التفاسير العربية:
يَقُولُ أَهۡلَكۡتُ مَالٗا لُّبَدًا
Yana cẽwa "Na* halakarda dũkiya mai yawa,"
* Nã halaka dukiya mai yawa dõmin faɗã da addĩni.
التفاسير العربية:
أَيَحۡسَبُ أَن لَّمۡ يَرَهُۥٓ أَحَدٌ
Shin, yana zaton cewa wani bai gan shi ba?
التفاسير العربية:
أَلَمۡ نَجۡعَل لَّهُۥ عَيۡنَيۡنِ
Shin, ba Mu sanya masa idãnu biyu ba?
التفاسير العربية:
وَلِسَانٗا وَشَفَتَيۡنِ
Da harshe, da leɓɓa biyu.
التفاسير العربية:
وَهَدَيۡنَٰهُ ٱلنَّجۡدَيۡنِ
Kuma ba Mu shiryar da shi ga hanyõyi* biyu ba?
* Hanyar alheri da ta sharri.
التفاسير العربية:
فَلَا ٱقۡتَحَمَ ٱلۡعَقَبَةَ
To, don mene ne bai shiga Aƙabã ba?
التفاسير العربية:
وَمَآ أَدۡرَىٰكَ مَا ٱلۡعَقَبَةُ
Kuma mene ne ya sanar da kai abin da ake cẽ wa Aƙabã?
التفاسير العربية:
فَكُّ رَقَبَةٍ
Ita ce fansar wuyan bãwa.
التفاسير العربية:
أَوۡ إِطۡعَٰمٞ فِي يَوۡمٖ ذِي مَسۡغَبَةٖ
Ko kuwa ciyarwa, a cikin yini ma'abũcin yunwa.
التفاسير العربية:
يَتِيمٗا ذَا مَقۡرَبَةٍ
Ga marãya ma'abũcin zumunta.
التفاسير العربية:
أَوۡ مِسۡكِينٗا ذَا مَتۡرَبَةٖ
Ko kuwa wani matalauci ma'abũcin turɓãya.
التفاسير العربية:
ثُمَّ كَانَ مِنَ ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلصَّبۡرِ وَتَوَاصَوۡاْ بِٱلۡمَرۡحَمَةِ
Sa'an nan kuma ya kasance daga waɗanda suka yi ĩmãni, kuma suka yi wa jũna wasiyya da yin haƙuri, kuma suka yi wa jũna wasiyya da tausayi.
التفاسير العربية:
أُوْلَٰٓئِكَ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَيۡمَنَةِ
Waɗannan ne ma'abũta albarka*
* Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da dãma, a Lãhira.
التفاسير العربية:
وَٱلَّذِينَ كَفَرُواْ بِـَٔايَٰتِنَا هُمۡ أَصۡحَٰبُ ٱلۡمَشۡـَٔمَةِ
Kuma waɗanda suka kãfirta da ãyõyin Mu, sũ ne ma'abũta shu'umci*
* Ko kuwa waɗanda ake bai wa takardunsu da hagu, a Lãhira.
التفاسير العربية:
عَلَيۡهِمۡ نَارٞ مُّؤۡصَدَةُۢ
A kansu akwai wata wuta abar kullewa.
التفاسير العربية:
 
ترجمة معاني سورة: البلد
فهرس السور رقم الصفحة
 
ترجمة معاني القرآن الكريم - الترجمة الهوساوية - أبو بكر جومي - فهرس التراجم

ترجمة معاني القرآن الكريم إلى اللغة الهوسا، ترجمها أبو بكر محمود جومي. تم تصويبها بإشراف مركز رواد الترجمة، ويتاح الإطلاع على الترجمة الأصلية لغرض إبداء الرأي والتقييم والتطوير المستمر.

إغلاق