Translation of the Meanings of the Noble Qur'an - Hausa language - Abu Bakr Jomy * - Translations’ Index

XML CSV Excel API
Please review the Terms and Policies

Translation of the meanings Ayah: (22) Surah: An-Noor
وَلَا يَأۡتَلِ أُوْلُواْ ٱلۡفَضۡلِ مِنكُمۡ وَٱلسَّعَةِ أَن يُؤۡتُوٓاْ أُوْلِي ٱلۡقُرۡبَىٰ وَٱلۡمَسَٰكِينَ وَٱلۡمُهَٰجِرِينَ فِي سَبِيلِ ٱللَّهِۖ وَلۡيَعۡفُواْ وَلۡيَصۡفَحُوٓاْۗ أَلَا تُحِبُّونَ أَن يَغۡفِرَ ٱللَّهُ لَكُمۡۚ وَٱللَّهُ غَفُورٞ رَّحِيمٌ
Kuma kada* ma'abũta falala daga gare ku da mawadãta su rantse ga rashin su bãyar da alhẽri ga ma'abũta zumunta da miskĩnai da muhãjirai, a cikin hanyar Allah. Kuma su yãfe, kuma su kau da kai. shin, bã ku son Allah Ya gãfarta muku, alhãli Allah Mai gãfara ne, Mai jin ƙai?
* Mai yin alheri dõmin Allah kada ya yanke shi daga wanda yake yi wa alherin nan, sabõda yã yi masa wani laifi, da ya shãfe shi ga mutuncinsa kõ dũkiyarsa. Sai ya yãfe, ya kau da kai, ya ci gaba da alherinsa dõmin Allah, kamar yadda Mistahu, wanda yake a cikin dangin Abũbakar As-siddiƙ ya shiga a cikin Hadĩsil Ifk alhãli kuwa Abũbakar ke ciyar da shi sabõda shi misĩkini ne da zumuntã kuma a tsakãninsu, sai Abũbakar ya gãfarta masa, kuma ya ci gaba da bã shi abin da yake bã shi. Haka sauran wuɗanda suka fãda a cikin wannan masifa, an yãfe musu a bãyan an yi musu haddin ƙazafi, sai dai wanda ya ɗauki mai girmansa, wãtau Ibn Ubayyu, shi kam ba a yi masa haddi ba dõmin Allah Ya yi masa alkawarin azãba mai tsanani a Lãhira. Watau Musulmi ake yi wa haddi dõmin ya tsarkaka.
Arabic explanations of the Qur’an:
 
Translation of the meanings Ayah: (22) Surah: An-Noor
Surahs’ Index Page Number
 
Translation of the Meanings of the Noble Qur'an - Hausa language - Abu Bakr Jomy - Translations’ Index

Translation of the Quran meanings into Hausa by Abu Bakr Mahmoud Jomy. Corrected by supervision of Rowwad Translation Center. The original translation is available for suggestions, continuous evaluation and development.

close