Translation of the Meanings of the Noble Qur'an - Hausa language - Abu Bakr Jomy * - Translations’ Index

XML CSV Excel API
Please review the Terms and Policies

Translation of the meanings Surah: Al-Qalam   Ayah:

Suratu Al'kalam

نٓۚ وَٱلۡقَلَمِ وَمَا يَسۡطُرُونَ
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
Arabic explanations of the Qur’an:
مَآ أَنتَ بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ بِمَجۡنُونٖ
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
Arabic explanations of the Qur’an:
وَإِنَّ لَكَ لَأَجۡرًا غَيۡرَ مَمۡنُونٖ
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
Arabic explanations of the Qur’an:
وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٖ
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
Arabic explanations of the Qur’an:
فَسَتُبۡصِرُ وَيُبۡصِرُونَ
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
Arabic explanations of the Qur’an:
بِأَييِّكُمُ ٱلۡمَفۡتُونُ
Ga wanenku haukã take.
Arabic explanations of the Qur’an:
إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkin Sa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
Arabic explanations of the Qur’an:
فَلَا تُطِعِ ٱلۡمُكَذِّبِينَ
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
Arabic explanations of the Qur’an:
وَدُّواْ لَوۡ تُدۡهِنُ فَيُدۡهِنُونَ
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
Arabic explanations of the Qur’an:
وَلَا تُطِعۡ كُلَّ حَلَّافٖ مَّهِينٍ
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
Arabic explanations of the Qur’an:
هَمَّازٖ مَّشَّآءِۭ بِنَمِيمٖ
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
Arabic explanations of the Qur’an:
مَّنَّاعٖ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٍ أَثِيمٍ
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
Arabic explanations of the Qur’an:
عُتُلِّۭ بَعۡدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
Arabic explanations of the Qur’an:
أَن كَانَ ذَا مَالٖ وَبَنِينَ
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
Arabic explanations of the Qur’an:
إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Idan ana karanta masa ãyõyin Mu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
Arabic explanations of the Qur’an:
سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلۡخُرۡطُومِ
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
Arabic explanations of the Qur’an:
إِنَّا بَلَوۡنَٰهُمۡ كَمَا بَلَوۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡجَنَّةِ إِذۡ أَقۡسَمُواْ لَيَصۡرِمُنَّهَا مُصۡبِحِينَ
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
Arabic explanations of the Qur’an:
وَلَا يَسۡتَثۡنُونَ
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
Arabic explanations of the Qur’an:
فَطَافَ عَلَيۡهَا طَآئِفٞ مِّن رَّبِّكَ وَهُمۡ نَآئِمُونَ
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
Arabic explanations of the Qur’an:
فَأَصۡبَحَتۡ كَٱلصَّرِيمِ
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
Arabic explanations of the Qur’an:
فَتَنَادَوۡاْ مُصۡبِحِينَ
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
Arabic explanations of the Qur’an:
أَنِ ٱغۡدُواْ عَلَىٰ حَرۡثِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰرِمِينَ
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
Arabic explanations of the Qur’an:
فَٱنطَلَقُواْ وَهُمۡ يَتَخَٰفَتُونَ
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
Arabic explanations of the Qur’an:
أَن لَّا يَدۡخُلَنَّهَا ٱلۡيَوۡمَ عَلَيۡكُم مِّسۡكِينٞ
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
Arabic explanations of the Qur’an:
وَغَدَوۡاْ عَلَىٰ حَرۡدٖ قَٰدِرِينَ
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
Arabic explanations of the Qur’an:
فَلَمَّا رَأَوۡهَا قَالُوٓاْ إِنَّا لَضَآلُّونَ
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
Arabic explanations of the Qur’an:
بَلۡ نَحۡنُ مَحۡرُومُونَ
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
Arabic explanations of the Qur’an:
قَالَ أَوۡسَطُهُمۡ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ لَوۡلَا تُسَبِّحُونَ
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
Arabic explanations of the Qur’an:
قَالُواْ سُبۡحَٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَٰلِمِينَ
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
Arabic explanations of the Qur’an:
فَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَلَٰوَمُونَ
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
Arabic explanations of the Qur’an:
قَالُواْ يَٰوَيۡلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَٰغِينَ
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
Arabic explanations of the Qur’an:
عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبۡدِلَنَا خَيۡرٗا مِّنۡهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
Arabic explanations of the Qur’an:
كَذَٰلِكَ ٱلۡعَذَابُۖ وَلَعَذَابُ ٱلۡأٓخِرَةِ أَكۡبَرُۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ
Haka dai azãbar* take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
* Irin wannan azãba ce za a yi wa Ƙuraishãwa, dangin Annabi, kamar yadda aka yi wa mãsu gonar lambu, wãto da suka tũba aka musanya musu da abin da ya fi abin da suka sãba sãmu. Wato an gayã wa Annabi ne lõkacin da danginsa suka kangare, suka ƙi shiga Musulunci, aka yi musu azãbar fari, da rashin ruwa shekara bakwai, Allah Ya gaya masa cewa, zã su musulunta, alheri ya kõma musu. Ya kuwa kõma, kamar yadda Allah Ya yi alkawari
Arabic explanations of the Qur’an:
إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّٰتِ ٱلنَّعِيمِ
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
Arabic explanations of the Qur’an:
أَفَنَجۡعَلُ ٱلۡمُسۡلِمِينَ كَٱلۡمُجۡرِمِينَ
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
Arabic explanations of the Qur’an:
مَا لَكُمۡ كَيۡفَ تَحۡكُمُونَ
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
Arabic explanations of the Qur’an:
أَمۡ لَكُمۡ كِتَٰبٞ فِيهِ تَدۡرُسُونَ
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
Arabic explanations of the Qur’an:
إِنَّ لَكُمۡ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
Arabic explanations of the Qur’an:
أَمۡ لَكُمۡ أَيۡمَٰنٌ عَلَيۡنَا بَٰلِغَةٌ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ إِنَّ لَكُمۡ لَمَا تَحۡكُمُونَ
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kan Mu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
Arabic explanations of the Qur’an:
سَلۡهُمۡ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
Arabic explanations of the Qur’an:
أَمۡ لَهُمۡ شُرَكَآءُ فَلۡيَأۡتُواْ بِشُرَكَآئِهِمۡ إِن كَانُواْ صَٰدِقِينَ
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
Arabic explanations of the Qur’an:
يَوۡمَ يُكۡشَفُ عَن سَاقٖ وَيُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ فَلَا يَسۡتَطِيعُونَ
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujada, sai bã zã su iyãwa ba.
Arabic explanations of the Qur’an:
خَٰشِعَةً أَبۡصَٰرُهُمۡ تَرۡهَقُهُمۡ ذِلَّةٞۖ وَقَدۡ كَانُواْ يُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ وَهُمۡ سَٰلِمُونَ
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
Arabic explanations of the Qur’an:
فَذَرۡنِي وَمَن يُكَذِّبُ بِهَٰذَا ٱلۡحَدِيثِۖ سَنَسۡتَدۡرِجُهُم مِّنۡ حَيۡثُ لَا يَعۡلَمُونَ
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
Arabic explanations of the Qur’an:
وَأُمۡلِي لَهُمۡۚ إِنَّ كَيۡدِي مَتِينٌ
Ina jinkirtã musu, lalle kaidi Na mai ƙarfi ne.
Arabic explanations of the Qur’an:
أَمۡ تَسۡـَٔلُهُمۡ أَجۡرٗا فَهُم مِّن مَّغۡرَمٖ مُّثۡقَلُونَ
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
Arabic explanations of the Qur’an:
أَمۡ عِندَهُمُ ٱلۡغَيۡبُ فَهُمۡ يَكۡتُبُونَ
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
Arabic explanations of the Qur’an:
فَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلۡحُوتِ إِذۡ نَادَىٰ وَهُوَ مَكۡظُومٞ
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
Arabic explanations of the Qur’an:
لَّوۡلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعۡمَةٞ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلۡعَرَآءِ وَهُوَ مَذۡمُومٞ
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
Arabic explanations of the Qur’an:
فَٱجۡتَبَٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّٰلِحِينَ
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
Arabic explanations of the Qur’an:
وَإِن يَكَادُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَيُزۡلِقُونَكَ بِأَبۡصَٰرِهِمۡ لَمَّا سَمِعُواْ ٱلذِّكۡرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُۥ لَمَجۡنُونٞ
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
Arabic explanations of the Qur’an:
وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكۡرٞ لِّلۡعَٰلَمِينَ
Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.
Arabic explanations of the Qur’an:
 
Translation of the meanings Surah: Al-Qalam
Surahs’ Index Page Number
 
Translation of the Meanings of the Noble Qur'an - Hausa language - Abu Bakr Jomy - Translations’ Index

Translation of the Quran meanings into Hausa by Abu Bakr Mahmoud Jomy. Corrected by supervision of Rowwad Translation Center. The original translation is available for suggestions, continuous evaluation and development.

close