ترجمهٔ معانی قرآن کریم - ترجمه ى هوساوى - ابوبكر جومى * - لیست ترجمه ها

XML CSV Excel API
Please review the Terms and Policies

ترجمهٔ معانی آیه: (121) سوره: سوره آل عمران
وَإِذۡ غَدَوۡتَ مِنۡ أَهۡلِكَ تُبَوِّئُ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ مَقَٰعِدَ لِلۡقِتَالِۗ وَٱللَّهُ سَمِيعٌ عَلِيمٌ
Kuma a lõkacin* da ka yi sauko daga iyãlanka kana zaunar da mũminai a wurãren zamadõmin yãƙi, kuma Allah Mai ji ne, Masani.
* Misãli ne ga cewa idan kun yi ĩmãni, kuma kun yi taƙawa, to, ƙullinsu bã ya cũtar da ku da kõme, dõmin abin da ya auku a Yãƙin Uhdu ya isa misãli ga cewa, sai kun karkace daga hanya sa'an nan wani abu zai sãme ku. Asalin maganar shĩ ne, Annabi yã fita Uhdu da mutum ɗari tara da hamsin kuma kãfirai sunã dubũ uku. Annabi ya sauka a Uhdu rãnar Asabat, bakwai ga Shawwal, shekara ta uku ga Hijira, ya sanya bayansa wajen dũtsen Uhdu, ya gyãra safũfuwan mayãƙa, kuma ya zaunar da wata runduna ta maharba a gefen dũtsen da shugabancin Abdullahi ɗan Jubair. Sa'an nan ya ce musu: "Ku kãre mu da harbi, kada su zo mana daga bãya, kada ku ɗaga daga nan, mun rinjãya kõ an rinjãye mu." Sai suka sãɓãwa umurnin, don haka masĩfar Uhdu ta auku.
تفسیرهای عربی:
 
ترجمهٔ معانی آیه: (121) سوره: سوره آل عمران
فهرست سوره ها شماره صفحه
 
ترجمهٔ معانی قرآن کریم - ترجمه ى هوساوى - ابوبكر جومى - لیست ترجمه ها

ترجمهٔ معانی قرآن کریم به زبان هوسا ـ برگردان: ابوبکر محمود جومی ـ مراجعه شده زیر نظر مرکز ترجمهٔ رواد. ترجمهٔ اصلی به هدف اظهار نظر و ارزش‌گذاری و بهبود مستمر در معرض نظر خوانندگان قرار دارد.

بستن