Ibisobanuro bya qoran ntagatifu - Ibisobanuro mu gihawusawiya - abubakar djumiy * - Ishakiro ry'ibisobanuro

XML CSV Excel API
Please review the Terms and Policies

Ibisobanuro by'amagambo Isura: Aswafati (Abari ku mirongo)   Umurongo:

Suratu Al'safat

وَٱلصَّٰٓفَّٰتِ صَفّٗا
Inã rantsuwa da mãsu yin sahu-sahu (a cikin salla kõ yãƙi).
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱلزَّٰجِرَٰتِ زَجۡرٗا
Sa'an nan mãsu yin tsãwa* dõmin gargaɗi.
* Mãsu tsãwa, sũ ne Malamai mãsu sãmun ilmin wa'azi daga Annabãwa waɗanda ke karãtun abin tunãwa daga Allah Ubangijin sammai da ƙasa, Mai bãyar da haske ga rãnã, Mai haskaka taurari mãsu ƙãwãtar da samã kuma su tsare ta daga shaiɗanu. An siffanta rãnã da Annabãwa, Malamai da taurãri, ilmi da haske da sababin ƙawa da shiryarwa da kõrar mãsu ɓarna.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱلتَّٰلِيَٰتِ ذِكۡرًا
Sa'an nan da mãsu karãtun abin tunãtarwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّ إِلَٰهَكُمۡ لَوَٰحِدٞ
Lalle Abin bautawarku haƙĩƙa ¦aya ne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
رَّبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَا وَرَبُّ ٱلۡمَشَٰرِقِ
Ubangijin sammai da ƙasã da abin da ke tsakãninsu, kuma Ubangijin wurãren fitar rãnã.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّا زَيَّنَّا ٱلسَّمَآءَ ٱلدُّنۡيَا بِزِينَةٍ ٱلۡكَوَاكِبِ
Lalle Mũ, Mun ƙãwatãr da sama ta kusa da wata ƙawa, watau taurãri.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَحِفۡظٗا مِّن كُلِّ شَيۡطَٰنٖ مَّارِدٖ
Kuma sunã tsari daga dukan Shaiɗan mai tsaurin kai.
Ibisobanuro by'icyarabu:
لَّا يَسَّمَّعُونَ إِلَى ٱلۡمَلَإِ ٱلۡأَعۡلَىٰ وَيُقۡذَفُونَ مِن كُلِّ جَانِبٖ
Bã zã su iya saurãre zuwa ga jama'a mafi ɗaukaka (Malã'iku) ba, kuma anã jĩfar su daga kõwane gẽfe.
Ibisobanuro by'icyarabu:
دُحُورٗاۖ وَلَهُمۡ عَذَابٞ وَاصِبٌ
Dõmin tunkuɗẽwa kuma sunã da wata azãba tabbatacciya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِلَّا مَنۡ خَطِفَ ٱلۡخَطۡفَةَ فَأَتۡبَعَهُۥ شِهَابٞ ثَاقِبٞ
Fãce wanda ya fizgi wata kalma, sai yũla mai haske ta bĩ shi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱسۡتَفۡتِهِمۡ أَهُمۡ أَشَدُّ خَلۡقًا أَم مَّنۡ خَلَقۡنَآۚ إِنَّا خَلَقۡنَٰهُم مِّن طِينٖ لَّازِبِۭ
Ka tambaye su: "Shin sũ ne mafi wuya ga halittawa, kõ, kuwa waɗanda Muka halitta?" Lalle Mũ, Mun halitta su daga lãkã mai ɗauri.
Ibisobanuro by'icyarabu:
بَلۡ عَجِبۡتَ وَيَسۡخَرُونَ
Ã'a, kã yi mãmãki, alhãli kuwa sunã ta yin izgili.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِذَا ذُكِّرُواْ لَا يَذۡكُرُونَ
Kuma idan aka tunãtar da su, bã su tunãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِذَا رَأَوۡاْ ءَايَةٗ يَسۡتَسۡخِرُونَ
Idan suka ga wata ãyã, sai su dinga yin izgili.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَقَالُوٓاْ إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا سِحۡرٞ مُّبِينٌ
Kuma su ce, "Wannnan bã kõme ba, fãce sihiri, ne bayyananne."
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَءِذَا مِتۡنَا وَكُنَّا تُرَابٗا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَبۡعُوثُونَ
"Shin, idan mun mutu, kuma muka kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle mũ tabbas waɗandaake tãyarwa ne?
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَوَءَابَآؤُنَا ٱلۡأَوَّلُونَ
"Ashe kõ da ubanninmu na farko?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
قُلۡ نَعَمۡ وَأَنتُمۡ دَٰخِرُونَ
Ka ce: "Na'am alhãli kuwa kunã ƙasƙantattu."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَإِنَّمَا هِيَ زَجۡرَةٞ وَٰحِدَةٞ فَإِذَا هُمۡ يَنظُرُونَ
Tsãwa guda kawai ce, sai gã su, sunã dũbi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَقَالُواْ يَٰوَيۡلَنَا هَٰذَا يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Kuma su ce: "Yã bonenmu! Wannan ita ce rãnar sakamako."
Ibisobanuro by'icyarabu:
هَٰذَا يَوۡمُ ٱلۡفَصۡلِ ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تُكَذِّبُونَ
Wannan ita ce rãnar rarrabẽwa wadda kuka kasance kuna ƙaryatãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
۞ ٱحۡشُرُواْ ٱلَّذِينَ ظَلَمُواْ وَأَزۡوَٰجَهُمۡ وَمَا كَانُواْ يَعۡبُدُونَ
Ku tãra waɗanda suka yi zãlunci, da abõkan haɗinsu, da abin da suka kasance sunã bautãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
مِن دُونِ ٱللَّهِ فَٱهۡدُوهُمۡ إِلَىٰ صِرَٰطِ ٱلۡجَحِيمِ
Wanin Allah, sabõda haka ku shiryar da su zuwa ga hanyar Jahĩm.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَقِفُوهُمۡۖ إِنَّهُم مَّسۡـُٔولُونَ
Kuma ku tsayar da su, lalle su, waɗanda ake yi wa tambaya ne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
مَا لَكُمۡ لَا تَنَاصَرُونَ
Me ya sãme ku, bã ku taimakon jũna?
Ibisobanuro by'icyarabu:
بَلۡ هُمُ ٱلۡيَوۡمَ مُسۡتَسۡلِمُونَ
Ã'a, sũ a yau, mãsu sallamãwa ne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَسَآءَلُونَ
Kuma sãshensu ya fuskanta ga sãshe, sunã tambayar jũna.
Ibisobanuro by'icyarabu:
قَالُوٓاْ إِنَّكُمۡ كُنتُمۡ تَأۡتُونَنَا عَنِ ٱلۡيَمِينِ
Suka ce: "Lalle kũ, kun kasance kunã jẽ mana daga wajen dãma (inda muka amince)."
Ibisobanuro by'icyarabu:
قَالُواْ بَل لَّمۡ تَكُونُواْ مُؤۡمِنِينَ
Suka ce: "Ã'a, ba ku kasance mũminai ba.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَمَا كَانَ لَنَا عَلَيۡكُم مِّن سُلۡطَٰنِۭۖ بَلۡ كُنتُمۡ قَوۡمٗا طَٰغِينَ
"Kuma wani dalĩli bai kasance ba gare mu a kanku. Ã'a, kun kasance mutãne ne mãsu kẽtare iyãka."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَحَقَّ عَلَيۡنَا قَوۡلُ رَبِّنَآۖ إِنَّا لَذَآئِقُونَ
"Sabõda haka maganar Ubangijinmu ta wajaba a kanmu. Lalle mũ, mãsu ɗanɗanãwa ne."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأَغۡوَيۡنَٰكُمۡ إِنَّا كُنَّا غَٰوِينَ
"Sabõda haka muka ɓatar da ku. Lalle mũ, mun kasance ɓatattu."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَإِنَّهُمۡ يَوۡمَئِذٖ فِي ٱلۡعَذَابِ مُشۡتَرِكُونَ
To lalle sũ a rãnar nan, mãsu tãrayya ne a cikin azãbar.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَفۡعَلُ بِٱلۡمُجۡرِمِينَ
Lalle Mũ, kamar haka Muke aikatãwa game, da mãsu laifi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّهُمۡ كَانُوٓاْ إِذَا قِيلَ لَهُمۡ لَآ إِلَٰهَ إِلَّا ٱللَّهُ يَسۡتَكۡبِرُونَ
Lalle sũ, sun kasance idan an ce musu: "Bãbu abin bautãwa, fãce Allah," sai su dõra girman kai.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَيَقُولُونَ أَئِنَّا لَتَارِكُوٓاْ ءَالِهَتِنَا لِشَاعِرٖ مَّجۡنُونِۭ
Kuma sunã cẽwa, "Shin, mũ lalle mãsu barin gumãkanmu ne, sabõda maganar wani mawãƙi mahaukaci?
Ibisobanuro by'icyarabu:
بَلۡ جَآءَ بِٱلۡحَقِّ وَصَدَّقَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Ã'a, yã zo da gaskiya kuma ya gaskata Manzanni.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّكُمۡ لَذَآئِقُواْ ٱلۡعَذَابِ ٱلۡأَلِيمِ
Lalle kũ, haƙĩƙa mãsu ɗanɗana azãba mai raɗaɗi ne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَمَا تُجۡزَوۡنَ إِلَّا مَا كُنتُمۡ تَعۡمَلُونَ
Kuma bã zã a sãka muku ba fãce da abin da kuka kasance kunã aikatãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أُوْلَٰٓئِكَ لَهُمۡ رِزۡقٞ مَّعۡلُومٞ
Waɗannan sunã da abinci sananne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَوَٰكِهُ وَهُم مُّكۡرَمُونَ
Ya'yan itãcen marmari, kuma sunã waɗanda ake girmamãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فِي جَنَّٰتِ ٱلنَّعِيمِ
A cikin gidãjen Aljannar ni'ima.
Ibisobanuro by'icyarabu:
عَلَىٰ سُرُرٖ مُّتَقَٰبِلِينَ
A kan karagu, sunã mãsu fuskantar jũna.
Ibisobanuro by'icyarabu:
يُطَافُ عَلَيۡهِم بِكَأۡسٖ مِّن مَّعِينِۭ
Anã kẽwayãwa a kansu da hinjãlan giya, ta daga waɗansu marẽmari.
Ibisobanuro by'icyarabu:
بَيۡضَآءَ لَذَّةٖ لِّلشَّٰرِبِينَ
Farã mai dãɗi ga mashãyan.
Ibisobanuro by'icyarabu:
لَا فِيهَا غَوۡلٞ وَلَا هُمۡ عَنۡهَا يُنزَفُونَ
A cikinta bãbu jirĩ kuma ba su zama mãsu mãye daga gare ta ba,
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَعِندَهُمۡ قَٰصِرَٰتُ ٱلطَّرۡفِ عِينٞ
Kuma a wurinsu, akwai mãtan aure mãsu taƙaita kallonsu, mãsu manyan idãnu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
كَأَنَّهُنَّ بَيۡضٞ مَّكۡنُونٞ
Kamar dai su ƙwai ne ɓõyayye.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَسَآءَلُونَ
Sai sãshensu ya fuskanta a kan sãshe, sunã tambayar jũna.
Ibisobanuro by'icyarabu:
قَالَ قَآئِلٞ مِّنۡهُمۡ إِنِّي كَانَ لِي قَرِينٞ
Wani mai magana daga cikinsu ya ce: "Lalle ni wani abõki ya kasance a gare ni (a dũniya)."
Ibisobanuro by'icyarabu:
يَقُولُ أَءِنَّكَ لَمِنَ ٱلۡمُصَدِّقِينَ
Yanã cewa, "Shin, kai lalle, kanã daga mãsu gaskatãwa ne?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَءِذَا مِتۡنَا وَكُنَّا تُرَابٗا وَعِظَٰمًا أَءِنَّا لَمَدِينُونَ
"Ashe, idan muka mutu, kuma muka, kasance turɓaya da kasũsuwa, ashe, lalle, mũ tabbas waɗanda ake sãka wa ne?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
قَالَ هَلۡ أَنتُم مُّطَّلِعُونَ
(Mai maganar) ya ce: "Shin, kõ ku, mãsu tsinkãya ne (mu gan shi)?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱطَّلَعَ فَرَءَاهُ فِي سَوَآءِ ٱلۡجَحِيمِ
Sai ya tsinkãya, sai ya gan shi a cikin tsakar Jahim.
Ibisobanuro by'icyarabu:
قَالَ تَٱللَّهِ إِن كِدتَّ لَتُرۡدِينِ
Ya ce (masa), "Wallahi, lalle, kã yi kusa, haƙĩƙã, ka halakãni."
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَلَوۡلَا نِعۡمَةُ رَبِّي لَكُنتُ مِنَ ٱلۡمُحۡضَرِينَ
"Kuma bã dõmin ni'imar Ubangijĩna ba, lalle, dã na kasance daga waɗanda ake halartarwa (tãre da kai a cikin wutã)."
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَفَمَا نَحۡنُ بِمَيِّتِينَ
"Shin fa, ba mu zama mãsu mutuwa ba."
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِلَّا مَوۡتَتَنَا ٱلۡأُولَىٰ وَمَا نَحۡنُ بِمُعَذَّبِينَ
"Sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake azabtarwa ba?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ
Lalle, wannan shĩ ne babban rabo mai girma.
Ibisobanuro by'icyarabu:
لِمِثۡلِ هَٰذَا فَلۡيَعۡمَلِ ٱلۡعَٰمِلُونَ
Sabõda irin wannan, sai mãsu aiki su yi ta aikatãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَذَٰلِكَ خَيۡرٞ نُّزُلًا أَمۡ شَجَرَةُ ٱلزَّقُّومِ
Shin wancan shĩ ne mafi zama alhẽri ga liyafa kõ itãciyar zaƙƙũm?
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّا جَعَلۡنَٰهَا فِتۡنَةٗ لِّلظَّٰلِمِينَ
Lalle, Mũ, Mun sanya ta fitina ga. azzãlumai.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّهَا شَجَرَةٞ تَخۡرُجُ فِيٓ أَصۡلِ ٱلۡجَحِيمِ
Lalle ita wata itãciya ce wadda take fita daga asalin Jahĩm.
Ibisobanuro by'icyarabu:
طَلۡعُهَا كَأَنَّهُۥ رُءُوسُ ٱلشَّيَٰطِينِ
Gundarta, kamar dai shi kãnun Shaiɗan ne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَإِنَّهُمۡ لَأٓكِلُونَ مِنۡهَا فَمَالِـُٔونَ مِنۡهَا ٱلۡبُطُونَ
To, lalle sũ haƙĩƙa mãsu ci ne daga gare ta. Sa'an nan mãsu cika cikuna ne daga gare ta.
Ibisobanuro by'icyarabu:
ثُمَّ إِنَّ لَهُمۡ عَلَيۡهَا لَشَوۡبٗا مِّنۡ حَمِيمٖ
Sa'an nan lalle sunã da wani garwaye a kanta, daga ruwan zãfi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
ثُمَّ إِنَّ مَرۡجِعَهُمۡ لَإِلَى ٱلۡجَحِيمِ
Sa'an nan lalle makomarsu, haƙĩƙa, zuwa ga Jãhĩm take.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّهُمۡ أَلۡفَوۡاْ ءَابَآءَهُمۡ ضَآلِّينَ
Lalle sũ, sun iske ubanninsu batattu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَهُمۡ عَلَىٰٓ ءَاثَٰرِهِمۡ يُهۡرَعُونَ
Sabõda haka sũ, a kan gurãbunsu, suke gaggãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَلَقَدۡ ضَلَّ قَبۡلَهُمۡ أَكۡثَرُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Kuma tabbas haƙĩƙa mafi yawan mutãnen farko sun ɓace a gabãninsu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَلَقَدۡ أَرۡسَلۡنَا فِيهِم مُّنذِرِينَ
Kuma tabbas haƙĩƙa, Mun aika mãsu gargaɗi a cikinsu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱنظُرۡ كَيۡفَ كَانَ عَٰقِبَةُ ٱلۡمُنذَرِينَ
Sai ka dũba yadda ãƙibar waɗanda aka yi wa gargaɗi ta kasance.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ
Fãce bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَلَقَدۡ نَادَىٰنَا نُوحٞ فَلَنِعۡمَ ٱلۡمُجِيبُونَ
Kuma lalle, haƙĩƙa' Nũhu ya kira Mu. To, madalla da mãsu karɓãwa, Mu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥ مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ
Kuma Mun tsĩrar da shi da mutãnensa daga bakin ciki babba.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَجَعَلۡنَا ذُرِّيَّتَهُۥ هُمُ ٱلۡبَاقِينَ
Muka sanya zurriyarsa sunã mãsu wanzuwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ
Kuma Muka bar masa (yabo) a cikin jama'ar ƙarshe.
Ibisobanuro by'icyarabu:
سَلَٰمٌ عَلَىٰ نُوحٖ فِي ٱلۡعَٰلَمِينَ
Aminci ya tabbata ga Nũhu, a cikin halittu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Lalle shi, yanã daga bãyin Mu mũminai.
Ibisobanuro by'icyarabu:
ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ
Sã'an nan Muka nutsar da waɗansunsu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
۞ وَإِنَّ مِن شِيعَتِهِۦ لَإِبۡرَٰهِيمَ
Kuma lalle daga ƙungiyarsa, haƙĩƙa, Ibrahĩm yake.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِذۡ جَآءَ رَبَّهُۥ بِقَلۡبٖ سَلِيمٍ
A lõkacin da ya je wa ubangijinsa da zũciya kuɓutacciya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِذۡ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوۡمِهِۦ مَاذَا تَعۡبُدُونَ
A lõkacin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bautãwa?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَئِفۡكًا ءَالِهَةٗ دُونَ ٱللَّهِ تُرِيدُونَ
"Shin, ƙiren ƙarya (wãtau) gumãka, wanin Allah, kuke bautãwa?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَمَا ظَنُّكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"To, mẽne ne zatonku game da Ubangijin halittu?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَنَظَرَ نَظۡرَةٗ فِي ٱلنُّجُومِ
Sai ya yi dũbi, dũba ta sõsai, a cikin taurãri.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَقَالَ إِنِّي سَقِيمٞ
Sã'an nan ya ce: "Nĩ mai rashin lãfiya ne."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَتَوَلَّوۡاْ عَنۡهُ مُدۡبِرِينَ
Sai suka jũya ga barinsa, sunã mãsu jũyãwa da bãya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَرَاغَ إِلَىٰٓ ءَالِهَتِهِمۡ فَقَالَ أَلَا تَأۡكُلُونَ
Sai ya karkata zuwa ga gumãkansu, sa'an nan ya ce: "Ashe bã zã ku ci ba?
Ibisobanuro by'icyarabu:
مَا لَكُمۡ لَا تَنطِقُونَ
"Me ya sãme ku, bã ku magana?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَرَاغَ عَلَيۡهِمۡ ضَرۡبَۢا بِٱلۡيَمِينِ
Sai ya zuba dũka a kansu da hannun dãma.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأَقۡبَلُوٓاْ إِلَيۡهِ يَزِفُّونَ
Sai suka fuskanto zuwa gare shi, sunã gaggãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
قَالَ أَتَعۡبُدُونَ مَا تَنۡحِتُونَ
Ya ce, "Kunã bauta wa abin da kuke sassaƙawa,
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَٱللَّهُ خَلَقَكُمۡ وَمَا تَعۡمَلُونَ
"Alhãli, Allah ne Ya halitta ku game da abin da kuke aikatãwa?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
قَالُواْ ٱبۡنُواْ لَهُۥ بُنۡيَٰنٗا فَأَلۡقُوهُ فِي ٱلۡجَحِيمِ
Suka ce: "Ku gina wani gini sabõda shi, sa'an nan ku jẽfa shi a cikin Jahĩm."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأَرَادُواْ بِهِۦ كَيۡدٗا فَجَعَلۡنَٰهُمُ ٱلۡأَسۡفَلِينَ
Sabõda haka suka yi nufin makĩda game da shi. Sai Muka sanya su, sũ ne mafi ƙasƙanci.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَقَالَ إِنِّي ذَاهِبٌ إِلَىٰ رَبِّي سَيَهۡدِينِ
Kuma (Ibrahĩm] ya ce: "Lalle, nĩ mai tafiya ne zuwa ga Ubangijĩna, zai shiryar da ni."
Ibisobanuro by'icyarabu:
رَبِّ هَبۡ لِي مِنَ ٱلصَّٰلِحِينَ
"Ya Ubangijĩna! Ka bã ni (abõkin zama) daga sãlihan mutãne."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَبَشَّرۡنَٰهُ بِغُلَٰمٍ حَلِيمٖ
Sai Muka yi masa bushãra da wani yãro *mai haƙuri.
* Yãron da aka yi bushãra da shi a nan, shĩ ne Ismã'ĩla' sabõda abin da yake tafe a gaba wanda ya shãfi Is'hãƙa da sũnansa a bayyane yã nũna a nan bã shi ba ne. Watau Ismã'ĩla kawai ne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَلَمَّا بَلَغَ مَعَهُ ٱلسَّعۡيَ قَالَ يَٰبُنَيَّ إِنِّيٓ أَرَىٰ فِي ٱلۡمَنَامِ أَنِّيٓ أَذۡبَحُكَ فَٱنظُرۡ مَاذَا تَرَىٰۚ قَالَ يَٰٓأَبَتِ ٱفۡعَلۡ مَا تُؤۡمَرُۖ سَتَجِدُنِيٓ إِن شَآءَ ٱللَّهُ مِنَ ٱلصَّٰبِرِينَ
To, a lõkacin da ya isa aiki tãre da shi, ya ce: "Ya ƙaramin ɗãna! Lalle ne inã gani, a ciki barci, lalle inã yanka ka. To, ka dũba mẽ ka gani?" (Yãron) ya ce: "Ya, Bãbãna! Ka aikata abin da aka umurce ka, zã ka sãme ni, in Allah Ya so, daga mãsu haƙuri."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَلَمَّآ أَسۡلَمَا وَتَلَّهُۥ لِلۡجَبِينِ
Yayin da suka mika wuya sai muka fansheshi da Rago @byakosowe
To, a lõkacin da suka yi sallama, (Ibrahĩm) ya kãyar da shi ga gẽfen gõshinsa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَنَٰدَيۡنَٰهُ أَن يَٰٓإِبۡرَٰهِيمُ
Kuma Muka kira shi cẽwa "Ya Ibrahĩm!"
Ibisobanuro by'icyarabu:
قَدۡ صَدَّقۡتَ ٱلرُّءۡيَآۚ إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ
"Haƙĩƙa kã gaskata mafarkin." Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّ هَٰذَا لَهُوَ ٱلۡبَلَٰٓؤُاْ ٱلۡمُبِينُ
Lalle wannan ita ce jarrabãwa bayyananna.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَفَدَيۡنَٰهُ بِذِبۡحٍ عَظِيمٖ
Kuma Muka yi fansar yãron da wani abin yanka, mai girma.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ
Kuma Muka bar (yabo) a kansa a cikin mutãnen ƙarshe.
Ibisobanuro by'icyarabu:
سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِبۡرَٰهِيمَ
Aminci ya tabbata ga Ibrãhĩm.
Ibisobanuro by'icyarabu:
كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ
Kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Lalle shĩ, yanã daga bãyinMu mũminai.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَبَشَّرۡنَٰهُ بِإِسۡحَٰقَ نَبِيّٗا مِّنَ ٱلصَّٰلِحِينَ
Kuma Muka yi masa bushãra* Da Is'hãƙa ya zama Annabi daga sãlihan mutãne.
* Wannan sãbuwar bushãra da Is'hãƙa tanã nũna cewa bã shĩ ne wanda kissar yankã ta shãfa ba sabõda haka Isma'ĩla dai ne tabbas, mai ƙissar yankã. Sabõda haka Allah Ya sanya shi wata al'umma dabam' dõmin a sãka masa, sa'an nan aka sãkawa Ibrãhĩm da Is'hãƙa dõmin ya zama wata al'umma ta dabam,.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَبَٰرَكۡنَا عَلَيۡهِ وَعَلَىٰٓ إِسۡحَٰقَۚ وَمِن ذُرِّيَّتِهِمَا مُحۡسِنٞ وَظَالِمٞ لِّنَفۡسِهِۦ مُبِينٞ
Kuma Muka yi albarka a gare shi, kuma ga Is'hãka. Kuma daga cikin zurriyarsu akwai mai kyautatãwa da kuma maizãlunci dõmin kansa, mai bayyanãwa (ga zãluncin).
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَلَقَدۡ مَنَنَّا عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ
Kuma lalle, Mun yi ni'ima ga Mũsã da Hãrũna.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَنَجَّيۡنَٰهُمَا وَقَوۡمَهُمَا مِنَ ٱلۡكَرۡبِ ٱلۡعَظِيمِ
Kuma Muka tsĩrar da su da mutãnensu daga bakin ciki mai girma.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَنَصَرۡنَٰهُمۡ فَكَانُواْ هُمُ ٱلۡغَٰلِبِينَ
Kuma Muka taimake su, sabõda haka suka kasance mãsu rinjãya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَءَاتَيۡنَٰهُمَا ٱلۡكِتَٰبَ ٱلۡمُسۡتَبِينَ
Kuma Muka ba su Littãfi mai iyãkar bayãni.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَهَدَيۡنَٰهُمَا ٱلصِّرَٰطَ ٱلۡمُسۡتَقِيمَ
Kuma Muka shiryar da su ga hanya mĩƙaƙƙiya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِمَا فِي ٱلۡأٓخِرِينَ
Kuma Muka bar (yabo) a gare su a cikin mutãnen karshe.
Ibisobanuro by'icyarabu:
سَلَٰمٌ عَلَىٰ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ
Aminci ya tabbata ga Mũsã da Hãruna.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ
Lalle kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّهُمَا مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Lalle, sunã daga bãyin Mu mũminai.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِنَّ إِلۡيَاسَ لَمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Kuma lalle Ilyãs, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِذۡ قَالَ لِقَوۡمِهِۦٓ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da yake ce wa mutãnensa, "Ashe, bã zã ku yi taƙawa ba?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَتَدۡعُونَ بَعۡلٗا وَتَذَرُونَ أَحۡسَنَ ٱلۡخَٰلِقِينَ
"Shin, kunã bauta wa Ba'al ne, kuma kunã barin Mafi kyautatãwar mãsu halitta?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
ٱللَّهَ رَبَّكُمۡ وَرَبَّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ
"Allah Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku farko?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَكَذَّبُوهُ فَإِنَّهُمۡ لَمُحۡضَرُونَ
Sai suka ƙaryata shi. Sabõda haka sũ lalle waɗanda zã a halartãwa ne (a wutã).
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَتَرَكۡنَا عَلَيۡهِ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ
Kuma Muka bar (yabo) a gare shi, a cikin mutãnen ƙarshe.
Ibisobanuro by'icyarabu:
سَلَٰمٌ عَلَىٰٓ إِلۡ يَاسِينَ
Aminci ya tabbata ga Ilyãs.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّا كَذَٰلِكَ نَجۡزِي ٱلۡمُحۡسِنِينَ
Lalle Mũ kamar haka Muke sãka wa mãsu kyautatãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّهُۥ مِنۡ عِبَادِنَا ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Lalle shĩ, yanã daga bãyin Mu mũminai.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِنَّ لُوطٗا لَّمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Kuma lalle Lũdu, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِذۡ نَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ
A lõkacin da Muka tsĩrar da shi, da mutãnensa gabã ɗaya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِلَّا عَجُوزٗا فِي ٱلۡغَٰبِرِينَ
Sai wata tsõhuwa tanã a cikin mãsu wanzuwa (a cikin azãba).
Ibisobanuro by'icyarabu:
ثُمَّ دَمَّرۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ
Sã'an nan Muka darkãke waɗansu mutãnen.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِنَّكُمۡ لَتَمُرُّونَ عَلَيۡهِم مُّصۡبِحِينَ
Kuma lalle kũ, haƙĩƙa, kunã shũɗewa a kansu, kunã mãsu asubanci.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَبِٱلَّيۡلِۚ أَفَلَا تَعۡقِلُونَ
Kuma da dare. Shin fa, bã zã ku hankalta ba?
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِنَّ يُونُسَ لَمِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Kuma lalle Yũnusa, haƙĩƙa, yanã daga Manzanni.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِذۡ أَبَقَ إِلَى ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ
A lõkacin da ya gudu zuwa ga jirgin ruwa wanda aka yi wa lõdi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَسَاهَمَ فَكَانَ مِنَ ٱلۡمُدۡحَضِينَ
Sã'an nan ya yi ƙuri'a, sai ya kasance a cikin waɗanda aka rinjaya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱلۡتَقَمَهُ ٱلۡحُوتُ وَهُوَ مُلِيمٞ
Sai kĩfi ya yi lõma da shi, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَلَوۡلَآ أَنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلۡمُسَبِّحِينَ
To, ba dõmin lalle shi ya kasance daga mãsu tasbĩhi ba,
Ibisobanuro by'icyarabu:
لَلَبِثَ فِي بَطۡنِهِۦٓ إِلَىٰ يَوۡمِ يُبۡعَثُونَ
Lalle dã ya zauna a cikin cikinsa har ya zuwa rãnar da zã a tãyar da su.
Ibisobanuro by'icyarabu:
۞ فَنَبَذۡنَٰهُ بِٱلۡعَرَآءِ وَهُوَ سَقِيمٞ
Sai Muka jẽfa shi ga wani fĩli alhãli kuwa yanã mai raunin rashin lãfiya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَأَنۢبَتۡنَا عَلَيۡهِ شَجَرَةٗ مِّن يَقۡطِينٖ
Kuma Muka tsirar da wata itãciya ta kankana a kusa da shi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَأَرۡسَلۡنَٰهُ إِلَىٰ مِاْئَةِ أَلۡفٍ أَوۡ يَزِيدُونَ
Kuma Muka aika shi zuwa ga waɗansu mutãne dubuɗari, kõ sunã ƙaruwa (a kan haka).
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَـَٔامَنُواْ فَمَتَّعۡنَٰهُمۡ إِلَىٰ حِينٖ
Sai suka yi ĩmãni sabõda haka Muka jiyar da su dãdi har wani lõkaci.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱسۡتَفۡتِهِمۡ أَلِرَبِّكَ ٱلۡبَنَاتُ وَلَهُمُ ٱلۡبَنُونَ
Sabõda haka, ka tambaye su, "Shin, Ubangijinka ne da 'ya'ya mãtã, kuma su da ɗiya maza?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَمۡ خَلَقۡنَا ٱلۡمَلَٰٓئِكَةَ إِنَٰثٗا وَهُمۡ شَٰهِدُونَ
Kõ kuma Mun halitta malã'iku mãtã ne, alhãli kuwa sũ sunãhalarce?
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَلَآ إِنَّهُم مِّنۡ إِفۡكِهِمۡ لَيَقُولُونَ
To! Lalle sũ, daga ƙiren ƙaryarsu sunã cẽwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَلَدَ ٱللَّهُ وَإِنَّهُمۡ لَكَٰذِبُونَ
"Allah Yã haihu," alhãli kuwa lalle sũ, haƙĩƙa maƙaryata ne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَصۡطَفَى ٱلۡبَنَاتِ عَلَى ٱلۡبَنِينَ
Shin, Yã zãɓi 'yã'ya mãtã ne a kan ɗiya maza?
Ibisobanuro by'icyarabu:
مَا لَكُمۡ كَيۡفَ تَحۡكُمُونَ
Mẽ ya same ku? Yãya kuke hukuntãwa (wannan hukunci)?
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَفَلَا تَذَكَّرُونَ
Shin, bã ku tunãni?
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَمۡ لَكُمۡ سُلۡطَٰنٞ مُّبِينٞ
Ko kuma kunã da wani dalĩli bayyananne ne?
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأۡتُواْ بِكِتَٰبِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ
To, ku zo da littãfinku idan kun kasance mãsu gaskiya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَجَعَلُواْ بَيۡنَهُۥ وَبَيۡنَ ٱلۡجِنَّةِ نَسَبٗاۚ وَلَقَدۡ عَلِمَتِ ٱلۡجِنَّةُ إِنَّهُمۡ لَمُحۡضَرُونَ
Kuma suka sanya nasaba a tsakãnin Sa da tsakãnin aljannu. Alhãli kuwa Lalle aljannu sun sani, "Lalle sũ, haƙĩƙa waɗanda ake halartarwa ne (a cikin wutã.)"
Ibisobanuro by'icyarabu:
سُبۡحَٰنَ ٱللَّهِ عَمَّا يَصِفُونَ
Tsarki ya tabbata ga Allah daga abin da suke siffantãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِلَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ
Sai bãyin Allah waɗanda aka tsarkake.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَإِنَّكُمۡ وَمَا تَعۡبُدُونَ
To, lalle, ku da abin da kuke bautãwa,
Ibisobanuro by'icyarabu:
مَآ أَنتُمۡ عَلَيۡهِ بِفَٰتِنِينَ
Ba ku zama mãsu buwãya ba a gare Shi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِلَّا مَنۡ هُوَ صَالِ ٱلۡجَحِيمِ
Sai wanda yake mai shiga babbar wutã Jahĩm.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَمَا مِنَّآ إِلَّا لَهُۥ مَقَامٞ مَّعۡلُومٞ
"Kuma bãbu kõwa daga cikinmu,* fãce yanã da matsayi sananne."
* Malã'iku da sauran halitta duka kõwa yã san matsayinsa na bauta ga Allah wanda ba Ya da dã ko diya, kuma ba Ya da dangantaka da kõwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِنَّا لَنَحۡنُ ٱلصَّآفُّونَ
"Kuma lalle mu, haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin sahu-sahu (dõmin ibãda)."
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِنَّا لَنَحۡنُ ٱلۡمُسَبِّحُونَ
"Kuma lalle mũ haƙĩƙa, mũ ne mãsu yin tasbĩhi."
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِن كَانُواْ لَيَقُولُونَ
Kuma lalle sũ, sun kasance sunã cẽwa,
Ibisobanuro by'icyarabu:
لَوۡ أَنَّ عِندَنَا ذِكۡرٗا مِّنَ ٱلۡأَوَّلِينَ
"Dã lalle munã da wani littãfi irin na mutãnen farko."
Ibisobanuro by'icyarabu:
لَكُنَّا عِبَادَ ٱللَّهِ ٱلۡمُخۡلَصِينَ
"Lalle dã mun kasance bãyin Allah waɗanda aka tsarkake."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَكَفَرُواْ بِهِۦۖ فَسَوۡفَ يَعۡلَمُونَ
Sai suka kãfirta da shi. Sabõda haka zã su sani.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَلَقَدۡ سَبَقَتۡ كَلِمَتُنَا لِعِبَادِنَا ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Kuma lalle, haƙĩƙa kalmar Mu ta gabãta ga bãyinMu, Manzanni.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّهُمۡ لَهُمُ ٱلۡمَنصُورُونَ
Lalle sũ, haƙĩƙa, sũ ne waɗanda ake taimako.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِنَّ جُندَنَا لَهُمُ ٱلۡغَٰلِبُونَ
Kuma lalle rundunarMu, haƙĩƙa, sũ ne marinjaya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَتَوَلَّ عَنۡهُمۡ حَتَّىٰ حِينٖ
Sabõda haka juya daga barinsu, har a wani lõkaci.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَأَبۡصِرۡهُمۡ فَسَوۡفَ يُبۡصِرُونَ
Ka nũna musu (gaskiya), da haka zã su dinga gani.*
* Wannan ƙãrin bayãni ne ga abin da sũrar ke karantarwa na cewa Annabãwa sũ ne kamar rãna mai haske na asali. Mãlamai kamar taurãri suke mãsu sãmun haske daga rana su wãtsa ga dũniya kuma su kõre ɓarna. Aya ta l79 da ke tafe karfafawa ce ga ma'anar wannan.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَفَبِعَذَابِنَا يَسۡتَعۡجِلُونَ
Shin fa, da azabarMu suke nẽman gaggãwa?
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَإِذَا نَزَلَ بِسَاحَتِهِمۡ فَسَآءَ صَبَاحُ ٱلۡمُنذَرِينَ
To, idan ta sauka ga farfãjiyarsu, to, sãfiyar wadanda ake yi wa gargaɗi ta mũnana.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَتَوَلَّ عَنۡهُمۡ حَتَّىٰ حِينٖ
Kuma ka jũya daga barinsu har a wani lõkaci.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَأَبۡصِرۡ فَسَوۡفَ يُبۡصِرُونَ
Ka nũna (musu gaskiya), da haka zã su dinga nũnãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
سُبۡحَٰنَ رَبِّكَ رَبِّ ٱلۡعِزَّةِ عَمَّا يَصِفُونَ
Tsarki ya tabbata ga Ubangijinka, Ubangijin rinjãye, daga barin abin da suke siffantãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَسَلَٰمٌ عَلَى ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Kuma aminci ya tabbata ga Manzanni.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَٱلۡحَمۡدُ لِلَّهِ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Kuma gõdiya ta tabbata ga Allah Ubangijin halittu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
 
Ibisobanuro by'amagambo Isura: Aswafati (Abari ku mirongo)
Urutonde rw'amasura numero y'urupapuro
 
Ibisobanuro bya qoran ntagatifu - Ibisobanuro mu gihawusawiya - abubakar djumiy - Ishakiro ry'ibisobanuro

ibisobanuro bya Qoraan ntagatifu mururimi rw'igihawusa byasobanuwe na Abuubakri Muhamudi Juumi byakosowe kd bihagararirwa nikigo rawaad tarjamat hagamijwe kugera kubisonuro byumwimerere no kungurana ibitekerezo niterambere rirambye

Gufunga