വിശുദ്ധ ഖുർആൻ പരിഭാഷ - ഹൗസാനിയൻ വിവർത്തനം - അബൂ ബക്‌ർ ജൂമീ. * - വിവർത്തനങ്ങളുടെ സൂചിക

XML CSV Excel API
Please review the Terms and Policies

പരിഭാഷ അദ്ധ്യായം: സൂറത്തുശ്ശുഅറാഅ്   ആയത്ത്:

Suratu Al'shu'araa

طسٓمٓ
T. S̃. M̃.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
لَعَلَّكَ بَٰخِعٞ نَّفۡسَكَ أَلَّا يَكُونُواْ مُؤۡمِنِينَ
Tsammãninka kai mai zaka halakar da ranka ne, dõn ba su zamanto mũminai ba! @തിരുത്തപ്പെട്ടത്
Tsammãninka kai mai halakar* da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!
* Wannan yã nũna cewa Annabi Muhammadu yanã jin tsõron rashin ĩmãnin mutãnensa, kada ya zama shĩ ne ya gajarta daga abin da Allah Ya ɗõra a kansa, na iyar da manzanci. Haka mũmini yake, kullum girman Ubangijinsa yake dũbi, sabõda haka kõme ya yi na ɗã'a, sai ya ga kãsãwar kansa ga tsayuwa da hakkin Ubangijinsa, a kansa, ya ƙãra jin tsõro da tawãli'u.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِن نَّشَأۡ نُنَزِّلۡ عَلَيۡهِم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ ءَايَةٗ فَظَلَّتۡ أَعۡنَٰقُهُمۡ لَهَا خَٰضِعِينَ
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَا يَأۡتِيهِم مِّن ذِكۡرٖ مِّنَ ٱلرَّحۡمَٰنِ مُحۡدَثٍ إِلَّا كَانُواْ عَنۡهُ مُعۡرِضِينَ
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَقَدۡ كَذَّبُواْ فَسَيَأۡتِيهِمۡ أَنۢبَٰٓؤُاْ مَا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ إِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَمۡ أَنۢبَتۡنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوۡجٖ كَرِيمٍ
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِذۡ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱئۡتِ ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّٰلِمِينَ
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَوۡمَ فِرۡعَوۡنَۚ أَلَا يَتَّقُونَ
"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ رَبِّ إِنِّيٓ أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَيَضِيقُ صَدۡرِي وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِي فَأَرۡسِلۡ إِلَىٰ هَٰرُونَ
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci* kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
* Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَلَهُمۡ عَلَيَّ ذَنۢبٞ فَأَخَافُ أَن يَقۡتُلُونِ
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ كَلَّاۖ فَٱذۡهَبَا بِـَٔايَٰتِنَآۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسۡتَمِعُونَ
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأۡتِيَا فِرۡعَوۡنَ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولُ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَنۡ أَرۡسِلۡ مَعَنَا بَنِيٓ إِسۡرَٰٓءِيلَ
"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ أَلَمۡ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدٗا وَلَبِثۡتَ فِينَا مِنۡ عُمُرِكَ سِنِينَ
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَفَعَلۡتَ فَعۡلَتَكَ ٱلَّتِي فَعَلۡتَ وَأَنتَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ
"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ فَعَلۡتُهَآ إِذٗا وَأَنَا۠ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin fushi." @തിരുത്തപ്പെട്ടത്
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَفَرَرۡتُ مِنكُمۡ لَمَّا خِفۡتُكُمۡ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكۡمٗا وَجَعَلَنِي مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَتِلۡكَ نِعۡمَةٞ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنۡ عَبَّدتَّ بَنِيٓ إِسۡرَٰٓءِيلَ
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ فِرۡعَوۡنُ وَمَا رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ رَبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ لِمَنۡ حَوۡلَهُۥٓ أَلَا تَسۡتَمِعُونَ
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ رَبُّكُمۡ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ ٱلَّذِيٓ أُرۡسِلَ إِلَيۡكُمۡ لَمَجۡنُونٞ
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ رَبُّ ٱلۡمَشۡرِقِ وَٱلۡمَغۡرِبِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُمۡ تَعۡقِلُونَ
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ لَئِنِ ٱتَّخَذۡتَ إِلَٰهًا غَيۡرِي لَأَجۡعَلَنَّكَ مِنَ ٱلۡمَسۡجُونِينَ
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ أَوَلَوۡ جِئۡتُكَ بِشَيۡءٖ مُّبِينٖ
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ فَأۡتِ بِهِۦٓ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّٰدِقِينَ
Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأَلۡقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ ثُعۡبَانٞ مُّبِينٞ
Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَنَزَعَ يَدَهُۥ فَإِذَا هِيَ بَيۡضَآءُ لِلنَّٰظِرِينَ
Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ لِلۡمَلَإِ حَوۡلَهُۥٓ إِنَّ هَٰذَا لَسَٰحِرٌ عَلِيمٞ
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
يُرِيدُ أَن يُخۡرِجَكُم مِّنۡ أَرۡضِكُم بِسِحۡرِهِۦ فَمَاذَا تَأۡمُرُونَ
"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالُوٓاْ أَرۡجِهۡ وَأَخَاهُ وَٱبۡعَثۡ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
يَأۡتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٖ
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَجُمِعَ ٱلسَّحَرَةُ لِمِيقَٰتِ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ
Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلۡ أَنتُم مُّجۡتَمِعُونَ
Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ ٱلسَّحَرَةَ إِن كَانُواْ هُمُ ٱلۡغَٰلِبِينَ
"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَلَمَّا جَآءَ ٱلسَّحَرَةُ قَالُواْ لِفِرۡعَوۡنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجۡرًا إِن كُنَّا نَحۡنُ ٱلۡغَٰلِبِينَ
To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ نَعَمۡ وَإِنَّكُمۡ إِذٗا لَّمِنَ ٱلۡمُقَرَّبِينَ
Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ لَهُم مُّوسَىٰٓ أَلۡقُواْ مَآ أَنتُم مُّلۡقُونَ
Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأَلۡقَوۡاْ حِبَالَهُمۡ وَعِصِيَّهُمۡ وَقَالُواْ بِعِزَّةِ فِرۡعَوۡنَ إِنَّا لَنَحۡنُ ٱلۡغَٰلِبُونَ
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأَلۡقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ تَلۡقَفُ مَا يَأۡفِكُونَ
Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأُلۡقِيَ ٱلسَّحَرَةُ سَٰجِدِينَ
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالُوٓاْ ءَامَنَّا بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
رَبِّ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ
"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ ءَامَنتُمۡ لَهُۥ قَبۡلَ أَنۡ ءَاذَنَ لَكُمۡۖ إِنَّهُۥ لَكَبِيرُكُمُ ٱلَّذِي عَلَّمَكُمُ ٱلسِّحۡرَ فَلَسَوۡفَ تَعۡلَمُونَۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيۡدِيَكُمۡ وَأَرۡجُلَكُم مِّنۡ خِلَٰفٖ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمۡ أَجۡمَعِينَ
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالُواْ لَا ضَيۡرَۖ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنَّا نَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَٰيَٰنَآ أَن كُنَّآ أَوَّلَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
۞ وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنۡ أَسۡرِ بِعِبَادِيٓ إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã* ne.
* Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأَرۡسَلَ فِرۡعَوۡنُ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ
Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنَّ هَٰٓؤُلَآءِ لَشِرۡذِمَةٞ قَلِيلُونَ
"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّهُمۡ لَنَا لَغَآئِظُونَ
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَٰذِرُونَ
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأَخۡرَجۡنَٰهُم مِّن جَنَّٰتٖ وَعُيُونٖ
Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَكُنُوزٖ وَمَقَامٖ كَرِيمٖ
Da taskõki da mazauni mai kyau.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
كَذَٰلِكَۖ وَأَوۡرَثۡنَٰهَا بَنِيٓ إِسۡرَٰٓءِيلَ
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأَتۡبَعُوهُم مُّشۡرِقِينَ
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَلَمَّا تَرَٰٓءَا ٱلۡجَمۡعَانِ قَالَ أَصۡحَٰبُ مُوسَىٰٓ إِنَّا لَمُدۡرَكُونَ
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ كَلَّآۖ إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهۡدِينِ
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni." @തിരുത്തപ്പെട്ടത്
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡبَحۡرَۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرۡقٖ كَٱلطَّوۡدِ ٱلۡعَظِيمِ
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge,* kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.
* Teku ta tsãge hanya gõma sha biyu a kan adadin danginBanĩ Isrãĩla. Suka bi suka wuce, sa'ilin nan aka nutsar daFir'auna, shi da jama'arsa, a cikin hanyõyin ruwan,.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَأَزۡلَفۡنَا ثَمَّ ٱلۡأٓخَرِينَ
Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَأَنجَيۡنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَٱتۡلُ عَلَيۡهِمۡ نَبَأَ إِبۡرَٰهِيمَ
Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِذۡ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوۡمِهِۦ مَا تَعۡبُدُونَ
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالُواْ نَعۡبُدُ أَصۡنَامٗا فَنَظَلُّ لَهَا عَٰكِفِينَ
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ هَلۡ يَسۡمَعُونَكُمۡ إِذۡ تَدۡعُونَ
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَوۡ يَنفَعُونَكُمۡ أَوۡ يَضُرُّونَ
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالُواْ بَلۡ وَجَدۡنَآ ءَابَآءَنَا كَذَٰلِكَ يَفۡعَلُونَ
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ أَفَرَءَيۡتُم مَّا كُنتُمۡ تَعۡبُدُونَ
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُمُ ٱلۡأَقۡدَمُونَ
"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَإِنَّهُمۡ عَدُوّٞ لِّيٓ إِلَّا رَبَّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
ٱلَّذِي خَلَقَنِي فَهُوَ يَهۡدِينِ
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَٱلَّذِي هُوَ يُطۡعِمُنِي وَيَسۡقِينِ
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِذَا مَرِضۡتُ فَهُوَ يَشۡفِينِ
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَٱلَّذِي يُمِيتُنِي ثُمَّ يُحۡيِينِ
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَٱلَّذِيٓ أَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لِي خَطِيٓـَٔتِي يَوۡمَ ٱلدِّينِ
"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
رَبِّ هَبۡ لِي حُكۡمٗا وَأَلۡحِقۡنِي بِٱلصَّٰلِحِينَ
"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَٱجۡعَل لِّي لِسَانَ صِدۡقٖ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya* a cikin mutãnen ƙarshe."
* Harshen gaskiya shĩ ne yabõ mai kyau. Mutãnen ƙarshe sũ ne Musulmi al'ummar Annabi Muhammadu, mãsu shaida ga annabawa da iyar da manzanci
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَٱجۡعَلۡنِي مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ ٱلنَّعِيمِ
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَٱغۡفِرۡ لِأَبِيٓ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَلَا تُخۡزِنِي يَوۡمَ يُبۡعَثُونَ
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
يَوۡمَ لَا يَنفَعُ مَالٞ وَلَا بَنُونَ
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِلَّا مَنۡ أَتَى ٱللَّهَ بِقَلۡبٖ سَلِيمٖ
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَأُزۡلِفَتِ ٱلۡجَنَّةُ لِلۡمُتَّقِينَ
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِلۡغَاوِينَ
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَقِيلَ لَهُمۡ أَيۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡبُدُونَ
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
مِن دُونِ ٱللَّهِ هَلۡ يَنصُرُونَكُمۡ أَوۡ يَنتَصِرُونَ
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَكُبۡكِبُواْ فِيهَا هُمۡ وَٱلۡغَاوُۥنَ
Sai aka kikkife su* a cikinta, su da halakakkun.
* Gumãkan, sũ da halakakku mabiyansu. Dukkan mai ɓatarda wani shĩ ne gunki ga mai bin sa halakakke.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَجُنُودُ إِبۡلِيسَ أَجۡمَعُونَ
Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالُواْ وَهُمۡ فِيهَا يَخۡتَصِمُونَ
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
تَٱللَّهِ إِن كُنَّا لَفِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٍ
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِذۡ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَآ أَضَلَّنَآ إِلَّا ٱلۡمُجۡرِمُونَ
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَمَا لَنَا مِن شَٰفِعِينَ
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٖ
"Kuma bã mu da abõki, masõyi."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَلَوۡ أَنَّ لَنَا كَرَّةٗ فَنَكُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
كَذَّبَتۡ قَوۡمُ نُوحٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da Dan uwansu Nuhu ya ce musu, "Bã zã ku ji tsoron Allah ba?" @തിരുത്തപ്പെട്ടത്
A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
۞ قَالُوٓاْ أَنُؤۡمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلۡأَرۡذَلُونَ
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ وَمَا عِلۡمِي بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنۡ حِسَابُهُمۡ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّيۖ لَوۡ تَشۡعُرُونَ
"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Ban zama mai kõre mũminai ba."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنۡ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٞ مُّبِينٞ
"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰنُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمَرۡجُومِينَ
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوۡمِي كَذَّبُونِ
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَٱفۡتَحۡ بَيۡنِي وَبَيۡنَهُمۡ فَتۡحٗا وَنَجِّنِي وَمَن مَّعِيَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأَنجَيۡنَٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِي ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا بَعۡدُ ٱلۡبَاقِينَ
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
كَذَّبَتۡ عَادٌ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَتَبۡنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ ءَايَةٗ تَعۡبَثُونَ
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo* a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
* Sitãdiyo shi ne gidan wasanni da Turanci, alãmã da Lãrabci.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمۡ تَخۡلُدُونَ
"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?*"
* Kõ kuma wurãren sanã'õ'i kamar masãƙoƙi irin na zãmanin nan.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِذَا بَطَشۡتُم بَطَشۡتُمۡ جَبَّارِينَ
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَٱتَّقُواْ ٱلَّذِيٓ أَمَدَّكُم بِمَا تَعۡلَمُونَ
"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَمَدَّكُم بِأَنۡعَٰمٖ وَبَنِينَ
"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَجَنَّٰتٖ وَعُيُونٍ
"Da gõnaki da marẽmari."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُمۡ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٖ
"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالُواْ سَوَآءٌ عَلَيۡنَآ أَوَعَظۡتَ أَمۡ لَمۡ تَكُن مِّنَ ٱلۡوَٰعِظِينَ
Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا خُلُقُ ٱلۡأَوَّلِينَ
"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen* mutãnen farko."
* Wãtau lãbarun mutãne waɗanda ba su ci gaba ba bã su son a yi rawa da nishãɗi. Anã karantawar ma'anar ƙaryar ta farko, watau wai tãtsũniya ce: a ce wai a hana ãyã akan tsaunuka dõmin wasanni. Suna nufi da ãya ko alãma gidãjen rawa da na nashãdi watau stadiyam da kasĩno.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَا نَحۡنُ بِمُعَذَّبِينَ
"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَكَذَّبُوهُ فَأَهۡلَكۡنَٰهُمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
كَذَّبَتۡ ثَمُودُ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ صَٰلِحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَتُتۡرَكُونَ فِي مَا هَٰهُنَآ ءَامِنِينَ
"Shin, anã barin ku* a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"
* Kuna zaton zã a bar ku a irin wannan ni'ima' Allah bã zai karɓi rãyukanku ba kuma Ya yi muku hisãbi a kanta? Kayya! Zã a yi muku hisãbi a bãyan kun mutu an tsayar da ku, dõmin hisãbin ayyukan da kuka yi.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فِي جَنَّٰتٖ وَعُيُونٖ
"A cikin gõnaki da marẽmari."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَزُرُوعٖ وَنَخۡلٖ طَلۡعُهَا هَضِيمٞ
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi* mãsu narkẽwa a ciki?"
* Hirtsi shi ne 'ya'yan itãce sãbabbi tun ba su nuna ba. Wãtau hirtsin gonakinsu idan an ci shi narkewã ya ke yi a cikin ciki, balle kuma 'ya'yan itãce nunannu.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَتَنۡحِتُونَ مِنَ ٱلۡجِبَالِ بُيُوتٗا فَٰرِهِينَ
"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَلَا تُطِيعُوٓاْ أَمۡرَ ٱلۡمُسۡرِفِينَ
"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
ٱلَّذِينَ يُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا يُصۡلِحُونَ
"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلۡمُسَحَّرِينَ
Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
مَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا فَأۡتِ بِـَٔايَةٍ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّٰدِقِينَ
"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ هَٰذِهِۦ نَاقَةٞ لَّهَا شِرۡبٞ وَلَكُمۡ شِرۡبُ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ
Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan* yini, kuma kunã da shan yini sasanne."
* Kuna zaton zã a bar ku a irin wannan ni'ima' Allah bã zai karɓi rãyukanku ba kuma Ya yi muku hisãbi a kanta? Kayya! Zã a yi muku hisãbi a bãyan kun mutu an tsayar da ku, dõmin hisãbin ayyukan da kuka yi.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٖ فَيَأۡخُذَكُمۡ عَذَابُ يَوۡمٍ عَظِيمٖ
"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَعَقَرُوهَا فَأَصۡبَحُواْ نَٰدِمِينَ
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأَخَذَهُمُ ٱلۡعَذَابُۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
كَذَّبَتۡ قَوۡمُ لُوطٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da ɗan'uwansu,* Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
* Lũɗu ɗan'uwansu ne na zaman gari da aure kawai. Asalinsa ɗan baffan Ibrãhĩm ne, sun tãso daga gabas, ƙasar Bãbila suka yi hijira, har ibrahĩm ya sauka Habrũna a ƙasar Shãm, Lũɗu kuwa ya sauka a sadũm da alƙaryunta.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَتَأۡتُونَ ٱلذُّكۡرَانَ مِنَ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمۡ رَبُّكُم مِّنۡ أَزۡوَٰجِكُمۚ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٌ عَادُونَ
"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰلُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمُخۡرَجِينَ
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ إِنِّي لِعَمَلِكُم مِّنَ ٱلۡقَالِينَ
Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
رَبِّ نَجِّنِي وَأَهۡلِي مِمَّا يَعۡمَلُونَ
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِلَّا عَجُوزٗا فِي ٱلۡغَٰبِرِينَ
Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
ثُمَّ دَمَّرۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ
Sa'an nan kuma Muka hallaka wasu. @തിരുത്തപ്പെട്ടത്
Sa'an nan kuma Muka darkãke wasu.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهِم مَّطَرٗاۖ فَسَآءَ مَطَرُ ٱلۡمُنذَرِينَ
Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
كَذَّبَ أَصۡحَٰبُ لۡـَٔيۡكَةِ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ شُعَيۡبٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
۞ أَوۡفُواْ ٱلۡكَيۡلَ وَلَا تَكُونُواْ مِنَ ٱلۡمُخۡسِرِينَ
"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَزِنُواْ بِٱلۡقِسۡطَاسِ ٱلۡمُسۡتَقِيمِ
"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَلَا تَبۡخَسُواْ ٱلنَّاسَ أَشۡيَآءَهُمۡ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ
"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَٱتَّقُواْ ٱلَّذِي خَلَقَكُمۡ وَٱلۡجِبِلَّةَ ٱلۡأَوَّلِينَ
"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلۡمُسَحَّرِينَ
Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ ٱلۡكَٰذِبِينَ
"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَأَسۡقِطۡ عَلَيۡنَا كِسَفٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّٰدِقِينَ
"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
قَالَ رَبِّيٓ أَعۡلَمُ بِمَا تَعۡمَلُونَ
Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمۡ عَذَابُ يَوۡمِ ٱلظُّلَّةِۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٍ
Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije* ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.
* An ruwaito cewa Allah Ya bũɗe musu ƙõfar Jahannama, zãfi ya hana su zama akõ'ina cikin gidãjensu, sa'an nan aka sanya girgije ya yi musu inuwa mai sanyi-sanyi har suka tãru a ciki, sa'an nan aka sanya girgijen ya kãma da wuta a kansu suka ƙõne kurmus kamar an gasa fãra. Suka kõma tõka kamar yadda suka nema daga Shu'aibu da a jefa musu ɓaɓɓake daga sama idan ya zama daga mãsu gaskiya.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّهُۥ لَتَنزِيلُ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
نَزَلَ بِهِ ٱلرُّوحُ ٱلۡأَمِينُ
Rũhi* amintacce ne ya sauka da shi.
* Rũhul Ƙudus, shi ne Jibirĩl, amincin Allah ya tabbata a gare shi.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
عَلَىٰ قَلۡبِكَ لِتَكُونَ مِنَ ٱلۡمُنذِرِينَ
A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
بِلِسَانٍ عَرَبِيّٖ مُّبِينٖ
Da harshe na Larabci mai bayãni.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَإِنَّهُۥ لَفِي زُبُرِ ٱلۡأَوَّلِينَ
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَوَلَمۡ يَكُن لَّهُمۡ ءَايَةً أَن يَعۡلَمَهُۥ عُلَمَٰٓؤُاْ بَنِيٓ إِسۡرَٰٓءِيلَ
Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَلَوۡ نَزَّلۡنَٰهُ عَلَىٰ بَعۡضِ ٱلۡأَعۡجَمِينَ
Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَقَرَأَهُۥ عَلَيۡهِم مَّا كَانُواْ بِهِۦ مُؤۡمِنِينَ
Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
كَذَٰلِكَ سَلَكۡنَٰهُ فِي قُلُوبِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ
Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
لَا يُؤۡمِنُونَ بِهِۦ حَتَّىٰ يَرَوُاْ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَلِيمَ
Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَيَأۡتِيَهُم بَغۡتَةٗ وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ
Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَيَقُولُواْ هَلۡ نَحۡنُ مُنظَرُونَ
Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَفَبِعَذَابِنَا يَسۡتَعۡجِلُونَ
Ashe, to, da azãbar Mu suke nẽman gaggãwa?
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَفَرَءَيۡتَ إِن مَّتَّعۡنَٰهُمۡ سِنِينَ
Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
ثُمَّ جَآءَهُم مَّا كَانُواْ يُوعَدُونَ
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
مَآ أَغۡنَىٰ عَنۡهُم مَّا كَانُواْ يُمَتَّعُونَ
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare* su.
* Dã an bã su lõkaci mai tsawo sunã jin dãɗi da rãyuwar dũniya a cikinsa, to, rãnar da mutuwa kõ azãbar Allah ta je gare su, wannan lõkacin bã zai tunkuɗe mutuwar kõ azabar ba daga gare su.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَآ أَهۡلَكۡنَا مِن قَرۡيَةٍ إِلَّا لَهَا مُنذِرُونَ
Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
ذِكۡرَىٰ وَمَا كُنَّا ظَٰلِمِينَ
Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَا تَنَزَّلَتۡ بِهِ ٱلشَّيَٰطِينُ
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَمَا يَنۢبَغِي لَهُمۡ وَمَا يَسۡتَطِيعُونَ
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنَّهُمۡ عَنِ ٱلسَّمۡعِ لَمَعۡزُولُونَ
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَلَا تَدۡعُ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ فَتَكُونَ مِنَ ٱلۡمُعَذَّبِينَ
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَأَنذِرۡ عَشِيرَتَكَ ٱلۡأَقۡرَبِينَ
Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَٱخۡفِضۡ جَنَاحَكَ لِمَنِ ٱتَّبَعَكَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Kuma ka sassauta fikãfikanka* ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.
* Ka zama mai tausayi ga mũminai waɗanda suka bĩ ka, ka yi musu kamar yadda kãzã take yi wa 'ya'yanta ƙanana a lõkacin sanyi, kõ kuwa idan zã su yi barci dõmin ta kãre su daga cũta.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
فَإِنۡ عَصَوۡكَ فَقُلۡ إِنِّي بَرِيٓءٞ مِّمَّا تَعۡمَلُونَ
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱلۡعَزِيزِ ٱلرَّحِيمِ
Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
ٱلَّذِي يَرَىٰكَ حِينَ تَقُومُ
Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَتَقَلُّبَكَ فِي ٱلسَّٰجِدِينَ
Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ
Lalle Shi, Shi* ne Mai ji, Masani.
* Allah Shi ne Mai ji, ji na gaskiya, kuma Masani, sani na gaskiya.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
هَلۡ أُنَبِّئُكُمۡ عَلَىٰ مَن تَنَزَّلُ ٱلشَّيَٰطِينُ
Shin, (kunã so) in gaya* muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?
* Wannan dõmin raddi ne gamãsu cewa aljannu ke gayawa Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, Alƙur'ãni. Aljannu bã su saukã sai ga maƙaryaci, mai zunubi' Muhammadu kuwa bã haka yake ba. Sabõda haka shi bã mahaukaci ba, kuma ba wanda aljannu suke gaya wa ba. Dukan abin da ya faɗa, to, wahayi ne daga Allah.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
تَنَزَّلُ عَلَىٰ كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٖ
Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
يُلۡقُونَ ٱلسَّمۡعَ وَأَكۡثَرُهُمۡ كَٰذِبُونَ
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَٱلشُّعَرَآءُ يَتَّبِعُهُمُ ٱلۡغَاوُۥنَ
Kuma mawãƙa* halakakku ne ke bin su.
* Siffõfin mawãƙa sun nũna cewa Annabi Muhammadu bã mawãƙi ba ne, dõmin bã shi da ɗaya daga cikin siffõfin mawãƙa. Kuma mabiyansa ba halakakku ba ne.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
أَلَمۡ تَرَ أَنَّهُمۡ فِي كُلِّ وَادٖ يَهِيمُونَ
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
وَأَنَّهُمۡ يَقُولُونَ مَا لَا يَفۡعَلُونَ
Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّٰلِحَٰتِ وَذَكَرُواْ ٱللَّهَ كَثِيرٗا وَٱنتَصَرُواْ مِنۢ بَعۡدِ مَا ظُلِمُواْۗ وَسَيَعۡلَمُ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ أَيَّ مُنقَلَبٖ يَنقَلِبُونَ
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.
അറബി ഖുർആൻ വിവരണങ്ങൾ:
 
പരിഭാഷ അദ്ധ്യായം: സൂറത്തുശ്ശുഅറാഅ്
സൂറത്തുകളുടെ സൂചിക പേജ് നമ്പർ
 
വിശുദ്ധ ഖുർആൻ പരിഭാഷ - ഹൗസാനിയൻ വിവർത്തനം - അബൂ ബക്‌ർ ജൂമീ. - വിവർത്തനങ്ങളുടെ സൂചിക

വിശുദ്ധ ഖുർആൻ ആശയ വിവർത്തനം ഹൌസാ ഭാഷയിൽ, അബൂബക്ർ മഹ്‌മൂദ്‌ ജൂമിയുടെ പരിഭാഷ, റുവ്വാദ് തർജ്ജമ കേന്ദ്രം തിരുത്തൽ നിർവഹിച്ചു, അഭിപ്രായം രേഖപ്പെടുത്താനും മൂല്യനിർണയത്തിനും തുടർന്നും വിപുലീകരിക്കാനുമുള്ള സൗകര്യത്തിന് അസ്സൽ പരിഭാഷയും വായിക്കാൻ സൗകര്യമുണ്ട്.

അടക്കുക