Firo maanaaji al-quraan tedduɗo oo - Firo hawsiiwo, Abuubakri Juumiy * - Tippudi firooji ɗii

XML CSV Excel API
Please review the Terms and Policies

Firo maanaaji Simoore: Simoore yimooɓe   Aaya:

Suratu Al'shu'araa

طسٓمٓ
T. S̃. M̃.
Faccirooji aarabeeji:
تِلۡكَ ءَايَٰتُ ٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ
Waɗancan ãyõyin Littãfi ne bayyananne.
Faccirooji aarabeeji:
لَعَلَّكَ بَٰخِعٞ نَّفۡسَكَ أَلَّا يَكُونُواْ مُؤۡمِنِينَ
Tsammãninka kai mai zaka halakar da ranka ne, dõn ba su zamanto mũminai ba! @Ko feewtinaa
Tsammãninka kai mai halakar* da ranka ne, dõmin ba su kasance mũminai ba!
* Wannan yã nũna cewa Annabi Muhammadu yanã jin tsõron rashin ĩmãnin mutãnensa, kada ya zama shĩ ne ya gajarta daga abin da Allah Ya ɗõra a kansa, na iyar da manzanci. Haka mũmini yake, kullum girman Ubangijinsa yake dũbi, sabõda haka kõme ya yi na ɗã'a, sai ya ga kãsãwar kansa ga tsayuwa da hakkin Ubangijinsa, a kansa, ya ƙãra jin tsõro da tawãli'u.
Faccirooji aarabeeji:
إِن نَّشَأۡ نُنَزِّلۡ عَلَيۡهِم مِّنَ ٱلسَّمَآءِ ءَايَةٗ فَظَلَّتۡ أَعۡنَٰقُهُمۡ لَهَا خَٰضِعِينَ
Idan Mun so zã Mu saukar, a kansu, da wata ãyã daga sama, sai wuyõyinsu su yini sabõda ita sunã mãsu ƙasƙantar da kai.
Faccirooji aarabeeji:
وَمَا يَأۡتِيهِم مِّن ذِكۡرٖ مِّنَ ٱلرَّحۡمَٰنِ مُحۡدَثٍ إِلَّا كَانُواْ عَنۡهُ مُعۡرِضِينَ
Kuma wata tunãtarwa ba ta jẽ musu ba, daga Mai rahama, sãbuwa, fãce sun kasance daga barinta sunã mãsu bijirẽwa.
Faccirooji aarabeeji:
فَقَدۡ كَذَّبُواْ فَسَيَأۡتِيهِمۡ أَنۢبَٰٓؤُاْ مَا كَانُواْ بِهِۦ يَسۡتَهۡزِءُونَ
To, lalle ne, sun ƙaryata, to, lãbãran abin da suka kasance sunã yi na izgili da shi zã ya je musu.
Faccirooji aarabeeji:
أَوَلَمۡ يَرَوۡاْ إِلَى ٱلۡأَرۡضِ كَمۡ أَنۢبَتۡنَا فِيهَا مِن كُلِّ زَوۡجٖ كَرِيمٍ
Shin, ba su dũba ba zuwa ga ƙasa, da yawa Muka tsirar a cikinta, daga dukan nau'i mai kyau?
Faccirooji aarabeeji:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mũminai ba.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai rahama.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِذۡ نَادَىٰ رَبُّكَ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱئۡتِ ٱلۡقَوۡمَ ٱلظَّٰلِمِينَ
Kuma a lõkacin da Ubangijinka Ya kirãyi Mũsã, "Ka je wa mutãnen nan azzãlumai.
Faccirooji aarabeeji:
قَوۡمَ فِرۡعَوۡنَۚ أَلَا يَتَّقُونَ
"Mutãnen Fir'auna bã zã su yi taƙawa ba?"
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ رَبِّ إِنِّيٓ أَخَافُ أَن يُكَذِّبُونِ
Ya ce: "Ya Ubangijĩna, nĩ inã tsõron su ƙaryata ni.
Faccirooji aarabeeji:
وَيَضِيقُ صَدۡرِي وَلَا يَنطَلِقُ لِسَانِي فَأَرۡسِلۡ إِلَىٰ هَٰرُونَ
"Kuma ƙirjĩna ya yi ƙunci* kuma harshẽna bã zai saku ba sabõda haka ka aika zuwa ga Harũna.
* Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.
Faccirooji aarabeeji:
وَلَهُمۡ عَلَيَّ ذَنۢبٞ فَأَخَافُ أَن يَقۡتُلُونِ
"Kuma sunã da wani laifi a kaina, sabõda haka inã tsõron kada su kashe ni."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ كَلَّاۖ فَٱذۡهَبَا بِـَٔايَٰتِنَآۖ إِنَّا مَعَكُم مُّسۡتَمِعُونَ
Ya ce: "Kayya! Ku tafi, kũ biyu, da ÃyõyinMu. Lalle ne, Munã tãre da ku Munã Mãsu saurãre."
Faccirooji aarabeeji:
فَأۡتِيَا فِرۡعَوۡنَ فَقُولَآ إِنَّا رَسُولُ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Sai ku je wa Fir'auna, sa'an nan ku ce, Lalle ne, mu, Manzannin Ubangijin halitta ne."
Faccirooji aarabeeji:
أَنۡ أَرۡسِلۡ مَعَنَا بَنِيٓ إِسۡرَٰٓءِيلَ
"Ka saki Banĩ Isrã'ila tãre da mu."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ أَلَمۡ نُرَبِّكَ فِينَا وَلِيدٗا وَلَبِثۡتَ فِينَا مِنۡ عُمُرِكَ سِنِينَ
Ya ce: "Shin, ba mu yi rẽnonka ba a cikinmu kanã jãrĩri, kuma ka zauna a cikinmu shẽkarudaga lõkacin rãyuwarka?"
Faccirooji aarabeeji:
وَفَعَلۡتَ فَعۡلَتَكَ ٱلَّتِي فَعَلۡتَ وَأَنتَ مِنَ ٱلۡكَٰفِرِينَ
"Kuma ka aikata aikinka wanda ka aikata alhãli kai kanã daga butulai?"
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ فَعَلۡتُهَآ إِذٗا وَأَنَا۠ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin fushi." @Ko feewtinaa
Ya ce: "Na aikata shi a lõkacin inã daga mãsu jãhilcin hushi."
Faccirooji aarabeeji:
فَفَرَرۡتُ مِنكُمۡ لَمَّا خِفۡتُكُمۡ فَوَهَبَ لِي رَبِّي حُكۡمٗا وَجَعَلَنِي مِنَ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
"Sabõda haka na gudu daga gãre ku a lõkacin da na ji tsõronku, sai Ubangijĩna Ya bã ni hukunci, kuma Ya sanya ni daga Manzanni."
Faccirooji aarabeeji:
وَتِلۡكَ نِعۡمَةٞ تَمُنُّهَا عَلَيَّ أَنۡ عَبَّدتَّ بَنِيٓ إِسۡرَٰٓءِيلَ
"Kuma waccan ni'ima ce, kanã gõrint a kaina, dõmin kã bautar da Banĩ Isrã'ĩla."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ فِرۡعَوۡنُ وَمَا رَبُّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Fir'auna ya ce: "Kuma mene ne Ubangijin halittu?"
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ رَبُّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
Ya ce: "Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu ƙarfin ĩmãni."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ لِمَنۡ حَوۡلَهُۥٓ أَلَا تَسۡتَمِعُونَ
Ya ce wa waɗanda suke a gẽfensa, "Bã za ku saurãra ba?"
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ رَبُّكُمۡ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Ya ce: "Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ إِنَّ رَسُولَكُمُ ٱلَّذِيٓ أُرۡسِلَ إِلَيۡكُمۡ لَمَجۡنُونٞ
Ya ce: "Lalle ne Manzonku, wanda aka aiko zuwa gare ku, haƙi ƙa, mahaukaci ne."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ رَبُّ ٱلۡمَشۡرِقِ وَٱلۡمَغۡرِبِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُمۡ تَعۡقِلُونَ
Ya ce: "Ubangijin mafitar rãnã da maɓũyarta da abin dayake a tsakaninsu, idan kun kasance kunã hankalta."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ لَئِنِ ٱتَّخَذۡتَ إِلَٰهًا غَيۡرِي لَأَجۡعَلَنَّكَ مِنَ ٱلۡمَسۡجُونِينَ
Ya ce: "Lalle ne idan ka riƙi wani abin bautãwa wanĩna haƙĩƙa, inã sanyã ka daga ɗaurarru."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ أَوَلَوۡ جِئۡتُكَ بِشَيۡءٖ مُّبِينٖ
Ya ce: "Ashe, kuma kõ dã nã zõ maka da wani, abu mai bayyanãwa?"
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ فَأۡتِ بِهِۦٓ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّٰدِقِينَ
Ya ce: "To, ka zõ da shi idan ka kasance daga, mãsu gaskiya."
Faccirooji aarabeeji:
فَأَلۡقَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ ثُعۡبَانٞ مُّبِينٞ
Sai ya jẽfa sandarsa, sai ga ta kumurci bayyananne.
Faccirooji aarabeeji:
وَنَزَعَ يَدَهُۥ فَإِذَا هِيَ بَيۡضَآءُ لِلنَّٰظِرِينَ
Kuma ya fizge hannunsa, sai ga shi fari ga mãsu kallo.
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ لِلۡمَلَإِ حَوۡلَهُۥٓ إِنَّ هَٰذَا لَسَٰحِرٌ عَلِيمٞ
(Fir'auna) ya ce ga mashãwarta a gẽfensa, "Lalle ne, wannan haƙĩƙa, masihirci ne, mai ilmi!
Faccirooji aarabeeji:
يُرِيدُ أَن يُخۡرِجَكُم مِّنۡ أَرۡضِكُم بِسِحۡرِهِۦ فَمَاذَا تَأۡمُرُونَ
"Yanã son ya fitar da ku daga ƙasarku game da sihirinSa. To mẽne ne kuke shãwartãwa?"
Faccirooji aarabeeji:
قَالُوٓاْ أَرۡجِهۡ وَأَخَاهُ وَٱبۡعَثۡ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ
Suka ce: "Ka jinkirtar da shi, shĩ da ɗan'uwansa, kuma ka aika mãsu gayya a cikin birãne."
Faccirooji aarabeeji:
يَأۡتُوكَ بِكُلِّ سَحَّارٍ عَلِيمٖ
"Zã su zõ maka da dukkan mai yawan sihiri masani."
Faccirooji aarabeeji:
فَجُمِعَ ٱلسَّحَرَةُ لِمِيقَٰتِ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ
Sai aka tãra masihirta dõmin ajalin yini sananne.
Faccirooji aarabeeji:
وَقِيلَ لِلنَّاسِ هَلۡ أَنتُم مُّجۡتَمِعُونَ
Kuma aka ce wa mutãne "Kõ kũ mãsu tãruwã ne?
Faccirooji aarabeeji:
لَعَلَّنَا نَتَّبِعُ ٱلسَّحَرَةَ إِن كَانُواْ هُمُ ٱلۡغَٰلِبِينَ
"Tsammãninmu mu bi masihirta, idan sun kasance sũ ne marinjãya."
Faccirooji aarabeeji:
فَلَمَّا جَآءَ ٱلسَّحَرَةُ قَالُواْ لِفِرۡعَوۡنَ أَئِنَّ لَنَا لَأَجۡرًا إِن كُنَّا نَحۡنُ ٱلۡغَٰلِبِينَ
To, a lõkacin da masihirta suka jẽ suka ce wa Fir'auna,"Shin, lalle ne, haƙĩƙa munã da ijãra idan mun kasance mũ ne marinjãya?"
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ نَعَمۡ وَإِنَّكُمۡ إِذٗا لَّمِنَ ٱلۡمُقَرَّبِينَ
Ya ce: "Na'am! Kuma lalle ne, kũ ne a lõkacin haƙĩƙa muƙarrabai."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ لَهُم مُّوسَىٰٓ أَلۡقُواْ مَآ أَنتُم مُّلۡقُونَ
Mũsã ya ce musu, "Ku jẽfa abin da kuke mãsu jẽfãwa."
Faccirooji aarabeeji:
فَأَلۡقَوۡاْ حِبَالَهُمۡ وَعِصِيَّهُمۡ وَقَالُواْ بِعِزَّةِ فِرۡعَوۡنَ إِنَّا لَنَحۡنُ ٱلۡغَٰلِبُونَ
Sai suka jẽfa igiyõyinsu, da sandunansu, kuma suka ce: "Da ƙarfin Fir'auna lalle ne mũ, haƙĩƙa, mũ ne marinjãya."
Faccirooji aarabeeji:
فَأَلۡقَىٰ مُوسَىٰ عَصَاهُ فَإِذَا هِيَ تَلۡقَفُ مَا يَأۡفِكُونَ
Sai Mũsa ya jẽfa sandarsa, sai ga ta tanã harhaɗe abin da suke yi na ƙarya.
Faccirooji aarabeeji:
فَأُلۡقِيَ ٱلسَّحَرَةُ سَٰجِدِينَ
Sai aka jẽfar da masihirta sunã mãsu sujada.
Faccirooji aarabeeji:
قَالُوٓاْ ءَامَنَّا بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Suka ce: "Mun yi ĩmãni da Ubangijin halitta."
Faccirooji aarabeeji:
رَبِّ مُوسَىٰ وَهَٰرُونَ
"Ubangijin Mũsa da Hãrũna."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ ءَامَنتُمۡ لَهُۥ قَبۡلَ أَنۡ ءَاذَنَ لَكُمۡۖ إِنَّهُۥ لَكَبِيرُكُمُ ٱلَّذِي عَلَّمَكُمُ ٱلسِّحۡرَ فَلَسَوۡفَ تَعۡلَمُونَۚ لَأُقَطِّعَنَّ أَيۡدِيَكُمۡ وَأَرۡجُلَكُم مِّنۡ خِلَٰفٖ وَلَأُصَلِّبَنَّكُمۡ أَجۡمَعِينَ
Ya ce: "Ashe, kun yi ĩmãni sabõda shĩ, a gabãnin in yi muku izni? Lalle ne shi, haƙĩƙa babbanku ne wanda ya kõya muku sihirin, to, zã ku sani. Lalle ne haƙĩƙa, zan kakkãtse hannuwanku da kafãfunku a tarnaƙi, kuma haƙĩƙa, zan tsĩrẽ ku gabã ɗaya."
Faccirooji aarabeeji:
قَالُواْ لَا ضَيۡرَۖ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا مُنقَلِبُونَ
Suka ce: "Bãbu wata cũta! Lalle ne mũ mãsu jũyãwa ne zuwa ga Ubangijinmu."
Faccirooji aarabeeji:
إِنَّا نَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لَنَا رَبُّنَا خَطَٰيَٰنَآ أَن كُنَّآ أَوَّلَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Lalle ne mu munã kwaɗayin Ubangijinmu, Ya gãfarta mana kurakuranmu dõmin mun kasance farkon mãsu ĩmãni."
Faccirooji aarabeeji:
۞ وَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنۡ أَسۡرِ بِعِبَادِيٓ إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ
Kuma Muka aika zuwa ga Mũsã cẽwa ka yi tafiyar dare da bãyiNa, lalle ne kũ waɗanda ake biyã* ne.
* Mũsa yanã nũna cewa, shi yanã jin tsõro kada ya zama ya gajarta wajen iyar da manzanci, dõmin shi mai saurin fushine, yanã neman a taimake shi ɗan'uwansa Hãrũna.Wannan ya yi kama da farkon sũrar inda Annabi, tshĩra da amincin Allah su tabbata a gare shi, ya nũna tsõron taƙaitãwa ga iyar da manzancin Allah zuwa ga mutãnensa dõmin haka ba su yi ĩmãni ba. Hãlin Annabawa duka ɗaya ne ga tsõron taƙaita aikin Ubangijinsu.
Faccirooji aarabeeji:
فَأَرۡسَلَ فِرۡعَوۡنُ فِي ٱلۡمَدَآئِنِ حَٰشِرِينَ
Sai Fir'auna ya aika mãsu gayya a cikin birãne.
Faccirooji aarabeeji:
إِنَّ هَٰٓؤُلَآءِ لَشِرۡذِمَةٞ قَلِيلُونَ
"Lalle ne, waɗannan, haƙĩƙa, ƙungiya ce kaɗan."
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّهُمۡ لَنَا لَغَآئِظُونَ
"Kuma lalle ne sũ, a gare Mu, Mãsu fusãtarwa ne."
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّا لَجَمِيعٌ حَٰذِرُونَ
"Kuma lalle ne mũ haƙĩƙa gabã ɗaya mãsu sauna ne."
Faccirooji aarabeeji:
فَأَخۡرَجۡنَٰهُم مِّن جَنَّٰتٖ وَعُيُونٖ
Sai Muka fitar da su daga gonaki da marẽmari.
Faccirooji aarabeeji:
وَكُنُوزٖ وَمَقَامٖ كَرِيمٖ
Da taskõki da mazauni mai kyau.
Faccirooji aarabeeji:
كَذَٰلِكَۖ وَأَوۡرَثۡنَٰهَا بَنِيٓ إِسۡرَٰٓءِيلَ
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da su ga Banĩ Isrãĩla.
Faccirooji aarabeeji:
فَأَتۡبَعُوهُم مُّشۡرِقِينَ
Sai suka bĩ su sunã mãsu fita a lõkacin hũdõwar rãnã.
Faccirooji aarabeeji:
فَلَمَّا تَرَٰٓءَا ٱلۡجَمۡعَانِ قَالَ أَصۡحَٰبُ مُوسَىٰٓ إِنَّا لَمُدۡرَكُونَ
Sa'an nan a lõkacin da jama'a biyu suka ga jũna, sai abõkan Mũsã suka ce: "Lalle ne mũ haƙĩ ƙa, waɗanda ake riska ne."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ كَلَّآۖ إِنَّ مَعِيَ رَبِّي سَيَهۡدِينِ
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni." @Ko feewtinaa
Ya ce: "Kayya! Lalle ne Ubangijina Yanã tare da ni, zai shiryar da ni."
Faccirooji aarabeeji:
فَأَوۡحَيۡنَآ إِلَىٰ مُوسَىٰٓ أَنِ ٱضۡرِب بِّعَصَاكَ ٱلۡبَحۡرَۖ فَٱنفَلَقَ فَكَانَ كُلُّ فِرۡقٖ كَٱلطَّوۡدِ ٱلۡعَظِيمِ
Sai Muka yi wahayi zuwa ga Mũsã cẽwa "Ka dõki tẽku da sandarka." Sai tẽku ta tsãge,* kõwane tsãgi ya kasance kamar falalen dũtse mai girma.
* Teku ta tsãge hanya gõma sha biyu a kan adadin danginBanĩ Isrãĩla. Suka bi suka wuce, sa'ilin nan aka nutsar daFir'auna, shi da jama'arsa, a cikin hanyõyin ruwan,.
Faccirooji aarabeeji:
وَأَزۡلَفۡنَا ثَمَّ ٱلۡأٓخَرِينَ
Kuma Muka kusantar da waɗansu mutãne a can.
Faccirooji aarabeeji:
وَأَنجَيۡنَا مُوسَىٰ وَمَن مَّعَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ
Kuma Muka tsĩrar da Mũsã da waɗanda suke tãre da shi gabã ɗaya.
Faccirooji aarabeeji:
ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ
Sa'an nan kuma Muka nutsar da waɗansu mutãnen.
Faccirooji aarabeeji:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne Ubangijinka, kaƙĩƙa, Shĩ ne Mabũwayi, Mai jin ƙai.
Faccirooji aarabeeji:
وَٱتۡلُ عَلَيۡهِمۡ نَبَأَ إِبۡرَٰهِيمَ
Kuma ka karanta, a kansu, lãbãrin Ibrãhĩm.
Faccirooji aarabeeji:
إِذۡ قَالَ لِأَبِيهِ وَقَوۡمِهِۦ مَا تَعۡبُدُونَ
A sã'ilin da ya ce wa ubansa da mutãnensa, "Mẽne ne kuke bauta wa?"
Faccirooji aarabeeji:
قَالُواْ نَعۡبُدُ أَصۡنَامٗا فَنَظَلُّ لَهَا عَٰكِفِينَ
Suka ce: "Munã bauta wa gumãka, sabõda haka munã yini mãsu lazimta a gare su."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ هَلۡ يَسۡمَعُونَكُمۡ إِذۡ تَدۡعُونَ
Ya ce: "Shin, sunã jin ku, a lõkacin da kuke kira?"
Faccirooji aarabeeji:
أَوۡ يَنفَعُونَكُمۡ أَوۡ يَضُرُّونَ
"Kõ kuwa sunã amfãnin ku, kõ sunã cũtar ku?"
Faccirooji aarabeeji:
قَالُواْ بَلۡ وَجَدۡنَآ ءَابَآءَنَا كَذَٰلِكَ يَفۡعَلُونَ
Suka ce: "Ã'a mun sãmĩ ubanninmu, kamar haka ne suke aikatãwa."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ أَفَرَءَيۡتُم مَّا كُنتُمۡ تَعۡبُدُونَ
Ya ce: "Shin to, kun ga abin da kuka kasance kunã bautã wa?"
Faccirooji aarabeeji:
أَنتُمۡ وَءَابَآؤُكُمُ ٱلۡأَقۡدَمُونَ
"Kũ da ubanninku mafi daɗẽwa?"
Faccirooji aarabeeji:
فَإِنَّهُمۡ عَدُوّٞ لِّيٓ إِلَّا رَبَّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"To lalle ne, sũ maƙiya ne a gare ni, fãce Ubangijin halittu."
Faccirooji aarabeeji:
ٱلَّذِي خَلَقَنِي فَهُوَ يَهۡدِينِ
"Wanda Ya halitta ni, sa'an nan Yanã shiryar da ni."
Faccirooji aarabeeji:
وَٱلَّذِي هُوَ يُطۡعِمُنِي وَيَسۡقِينِ
"Kuma Wanda Yake Shĩ ne Yake ciyar da ni, kuma Yanã shãyar da ni."
Faccirooji aarabeeji:
وَإِذَا مَرِضۡتُ فَهُوَ يَشۡفِينِ
"Kuma idan na yi jiyya, to, Shĩ ne Yake warkar da ni."
Faccirooji aarabeeji:
وَٱلَّذِي يُمِيتُنِي ثُمَّ يُحۡيِينِ
"Kuma wanda Yake matar da ni, sa'an nan Ya rãyar da ni."
Faccirooji aarabeeji:
وَٱلَّذِيٓ أَطۡمَعُ أَن يَغۡفِرَ لِي خَطِيٓـَٔتِي يَوۡمَ ٱلدِّينِ
"Kuma wanda Yake inã kwaɗayin Ya gãfarta mini kurãkuraina, a rãnar sãkamako."
Faccirooji aarabeeji:
رَبِّ هَبۡ لِي حُكۡمٗا وَأَلۡحِقۡنِي بِٱلصَّٰلِحِينَ
"Ya Ubangijĩna! Ka ba ni hukunci, kuma Ka riskar da ni ga sãlihai."
Faccirooji aarabeeji:
وَٱجۡعَل لِّي لِسَانَ صِدۡقٖ فِي ٱلۡأٓخِرِينَ
"Kuma Ka sanya mini harshen gaskiya* a cikin mutãnen ƙarshe."
* Harshen gaskiya shĩ ne yabõ mai kyau. Mutãnen ƙarshe sũ ne Musulmi al'ummar Annabi Muhammadu, mãsu shaida ga annabawa da iyar da manzanci
Faccirooji aarabeeji:
وَٱجۡعَلۡنِي مِن وَرَثَةِ جَنَّةِ ٱلنَّعِيمِ
"Kuma Ka sanya ni daga magãdan Aljannar ni'ima."
Faccirooji aarabeeji:
وَٱغۡفِرۡ لِأَبِيٓ إِنَّهُۥ كَانَ مِنَ ٱلضَّآلِّينَ
"Kuma Ka gãfarta wa ubãna, lalle ne shi, ya kasance daga ɓatattu."
Faccirooji aarabeeji:
وَلَا تُخۡزِنِي يَوۡمَ يُبۡعَثُونَ
"Kuma kada Ka kunyata ni a rãnar da ake tãyar da su."
Faccirooji aarabeeji:
يَوۡمَ لَا يَنفَعُ مَالٞ وَلَا بَنُونَ
"A rãnar da dũkiya bã ta amfãni, kuma ɗiya bã su yi."
Faccirooji aarabeeji:
إِلَّا مَنۡ أَتَى ٱللَّهَ بِقَلۡبٖ سَلِيمٖ
"Fãce wanda ya jẽ wa Allah da zũciya mai tsarki."
Faccirooji aarabeeji:
وَأُزۡلِفَتِ ٱلۡجَنَّةُ لِلۡمُتَّقِينَ
Kuma aka kusantar da Aljanna ga mãsu taƙawa.
Faccirooji aarabeeji:
وَبُرِّزَتِ ٱلۡجَحِيمُ لِلۡغَاوِينَ
Kuma aka fitar da wutã babba dõmin halakakku.
Faccirooji aarabeeji:
وَقِيلَ لَهُمۡ أَيۡنَ مَا كُنتُمۡ تَعۡبُدُونَ
Kuma aka ce musu, "Inã abin da kuka kasance kunã bautawa?"
Faccirooji aarabeeji:
مِن دُونِ ٱللَّهِ هَلۡ يَنصُرُونَكُمۡ أَوۡ يَنتَصِرُونَ
"Baicin Allah? Shin sunã tamakon ku kõ kuwa sunã tsare kansu?"
Faccirooji aarabeeji:
فَكُبۡكِبُواْ فِيهَا هُمۡ وَٱلۡغَاوُۥنَ
Sai aka kikkife su* a cikinta, su da halakakkun.
* Gumãkan, sũ da halakakku mabiyansu. Dukkan mai ɓatarda wani shĩ ne gunki ga mai bin sa halakakke.
Faccirooji aarabeeji:
وَجُنُودُ إِبۡلِيسَ أَجۡمَعُونَ
Da rundunar Ibilĩsa gabã ɗaya.
Faccirooji aarabeeji:
قَالُواْ وَهُمۡ فِيهَا يَخۡتَصِمُونَ
Suka ce: alhãli sunã a cikinta sunã yin husũma,
Faccirooji aarabeeji:
تَٱللَّهِ إِن كُنَّا لَفِي ضَلَٰلٖ مُّبِينٍ
"Rantsuwa da Allah! Lalle ne mun kasance, haƙĩƙa, a cikin ɓata bayyananna."
Faccirooji aarabeeji:
إِذۡ نُسَوِّيكُم بِرَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"A lõkacin da muke daidaita ku da Ubangijin halittu.
Faccirooji aarabeeji:
وَمَآ أَضَلَّنَآ إِلَّا ٱلۡمُجۡرِمُونَ
"Kuma bãbu abin da ya ɓatar da mu fãce mãsu laifi."
Faccirooji aarabeeji:
فَمَا لَنَا مِن شَٰفِعِينَ
"Sabõda haka bã mu da waɗansu macẽta."
Faccirooji aarabeeji:
وَلَا صَدِيقٍ حَمِيمٖ
"Kuma bã mu da abõki, masõyi."
Faccirooji aarabeeji:
فَلَوۡ أَنَّ لَنَا كَرَّةٗ فَنَكُونَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Sabõda haka dã lalle munã da (dãmar) kõmawa, dõmin mu kasance daga mũminai!"
Faccirooji aarabeeji:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne, a cikin wancan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, bã su kasance mũminai ba.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Faccirooji aarabeeji:
كَذَّبَتۡ قَوۡمُ نُوحٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Mutãnen Nũhu sun ƙaryata Manzanni.
Faccirooji aarabeeji:
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ نُوحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da Dan uwansu Nuhu ya ce musu, "Bã zã ku ji tsoron Allah ba?" @Ko feewtinaa
A lõkacin da ɗan'uwansu, Nũhu, ya ce musu, "Shin, bã zã ku yi taƙawa ba?"
Faccirooji aarabeeji:
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne, zuwa gare ku, ni Manzo ne amintacce."
Faccirooji aarabeeji:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"To, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Faccirooji aarabeeji:
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãtã ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
Faccirooji aarabeeji:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka, ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Faccirooji aarabeeji:
۞ قَالُوٓاْ أَنُؤۡمِنُ لَكَ وَٱتَّبَعَكَ ٱلۡأَرۡذَلُونَ
Suka ce: "Ashe, zã mu yi ĩmãni sabõda kai alhãli kuwa mafiya ƙasƙanci sun bi ka?"
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ وَمَا عِلۡمِي بِمَا كَانُواْ يَعۡمَلُونَ
Ya ce: "Kuma bã ni da sani ga abin da suka kasance sanã aikatãwa."
Faccirooji aarabeeji:
إِنۡ حِسَابُهُمۡ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّيۖ لَوۡ تَشۡعُرُونَ
"Hisãbinsu bai zama ba fãce ga Ubangijina, dã kunã sansancẽwa."
Faccirooji aarabeeji:
وَمَآ أَنَا۠ بِطَارِدِ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Ban zama mai kõre mũminai ba."
Faccirooji aarabeeji:
إِنۡ أَنَا۠ إِلَّا نَذِيرٞ مُّبِينٞ
"Nĩ ba kõwa ba ne sai mai gargaɗi mai bayyanãwa."
Faccirooji aarabeeji:
قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰنُوحُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمَرۡجُومِينَ
Suka ce: "Lalle ne, idan ba ka hanu ba, yã Nũhu, (daga maganarka,) haƙĩƙa, kanã kasancẽwa daga waɗanda ake jẽfewa"
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ رَبِّ إِنَّ قَوۡمِي كَذَّبُونِ
Ya ce: "Yã Ubangijĩna! Lalle ne mutãnena sun ƙaryatã ni."
Faccirooji aarabeeji:
فَٱفۡتَحۡ بَيۡنِي وَبَيۡنَهُمۡ فَتۡحٗا وَنَجِّنِي وَمَن مَّعِيَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
"Sai ka yi hukunci, a tsakãnĩna da tsakãninsu tabbataccen hukanci, kuma ka tsĩrar da ni, da waɗanda suke tãre da ni daga mũminai."
Faccirooji aarabeeji:
فَأَنجَيۡنَٰهُ وَمَن مَّعَهُۥ فِي ٱلۡفُلۡكِ ٱلۡمَشۡحُونِ
Sai Muka tsĩrar da shi, shi da waɗanda suke tãre da shi, a cikin jirgi wanda aka yi wa lõdi.
Faccirooji aarabeeji:
ثُمَّ أَغۡرَقۡنَا بَعۡدُ ٱلۡبَاقِينَ
Sa'an nan Muka nutsar a bãyan haka, da sauran.
Faccirooji aarabeeji:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma Lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai Rahama.
Faccirooji aarabeeji:
كَذَّبَتۡ عَادٌ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Ãdãwa sun ƙaryata Manzanni.
Faccirooji aarabeeji:
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ هُودٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da ɗan'uwansu, Hũdu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
Faccirooji aarabeeji:
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, haƙĩƙa, Manzo ne, amintacce."
Faccirooji aarabeeji:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Faccirooji aarabeeji:
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Kuma bã ni tambayar wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba, fãce daga Ubangijin halittu."
Faccirooji aarabeeji:
أَتَبۡنُونَ بِكُلِّ رِيعٍ ءَايَةٗ تَعۡبَثُونَ
"Shin, kunã yin ginin sitadiyo* a kõwane tsauni ne, kunã yin wãsa?"
* Sitãdiyo shi ne gidan wasanni da Turanci, alãmã da Lãrabci.
Faccirooji aarabeeji:
وَتَتَّخِذُونَ مَصَانِعَ لَعَلَّكُمۡ تَخۡلُدُونَ
"Kuma kunã riƙon matsãrar ruwa, tsammãninku, ku dawwama?*"
* Kõ kuma wurãren sanã'õ'i kamar masãƙoƙi irin na zãmanin nan.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِذَا بَطَشۡتُم بَطَشۡتُمۡ جَبَّارِينَ
"Kuma idan kun yi damƙa, sai ku yi damƙar kunã mãsu tanƙwasãwa."
Faccirooji aarabeeji:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"To ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Faccirooji aarabeeji:
وَٱتَّقُواْ ٱلَّذِيٓ أَمَدَّكُم بِمَا تَعۡلَمُونَ
"Ku ji tsõron wanda Ya taimake ku da abin da kuka sani."
Faccirooji aarabeeji:
أَمَدَّكُم بِأَنۡعَٰمٖ وَبَنِينَ
"Ya taimake ku da dabbõbin ni'ima da ɗiya."
Faccirooji aarabeeji:
وَجَنَّٰتٖ وَعُيُونٍ
"Da gõnaki da marẽmari."
Faccirooji aarabeeji:
إِنِّيٓ أَخَافُ عَلَيۡكُمۡ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٖ
"Lalle ne nĩ, inã ji muku tsõron azãbar wani yini mai girma."
Faccirooji aarabeeji:
قَالُواْ سَوَآءٌ عَلَيۡنَآ أَوَعَظۡتَ أَمۡ لَمۡ تَكُن مِّنَ ٱلۡوَٰعِظِينَ
Suka ce: "Daidai ne a kanmu: Kã yi wa'azi kõ ba ka kasance daga mãsu wa'azi ba."
Faccirooji aarabeeji:
إِنۡ هَٰذَآ إِلَّا خُلُقُ ٱلۡأَوَّلِينَ
"Wannan abu bai zamõ ba fãce hãlãyen* mutãnen farko."
* Wãtau lãbarun mutãne waɗanda ba su ci gaba ba bã su son a yi rawa da nishãɗi. Anã karantawar ma'anar ƙaryar ta farko, watau wai tãtsũniya ce: a ce wai a hana ãyã akan tsaunuka dõmin wasanni. Suna nufi da ãya ko alãma gidãjen rawa da na nashãdi watau stadiyam da kasĩno.
Faccirooji aarabeeji:
وَمَا نَحۡنُ بِمُعَذَّبِينَ
"Kuma mũ ba mu zama waɗanda ake yi wa azãba ba."
Faccirooji aarabeeji:
فَكَذَّبُوهُ فَأَهۡلَكۡنَٰهُمۡۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Sabõda haka suka ƙaryata shi, sai Muka halakar da sũ. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne, Ubangijinka, haƙĩƙa, Shi ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Faccirooji aarabeeji:
كَذَّبَتۡ ثَمُودُ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Samũdãwa sun ƙaryata Manzanni.
Faccirooji aarabeeji:
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ صَٰلِحٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da ɗan'uwansu Sãlihu ya ce: "Shin, bã zã ku bi Allah da taƙawa ba?"
Faccirooji aarabeeji:
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne nĩ zuwã gare ku, Manzo ne, amintacce."
Faccirooji aarabeeji:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã.
Faccirooji aarabeeji:
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrãta ba ta zama ba fãce da a Ubangijin halittu."
Faccirooji aarabeeji:
أَتُتۡرَكُونَ فِي مَا هَٰهُنَآ ءَامِنِينَ
"Shin, anã barin ku* a cikin abin da yake a nan, kunã amintattu?"
* Kuna zaton zã a bar ku a irin wannan ni'ima' Allah bã zai karɓi rãyukanku ba kuma Ya yi muku hisãbi a kanta? Kayya! Zã a yi muku hisãbi a bãyan kun mutu an tsayar da ku, dõmin hisãbin ayyukan da kuka yi.
Faccirooji aarabeeji:
فِي جَنَّٰتٖ وَعُيُونٖ
"A cikin gõnaki da marẽmari."
Faccirooji aarabeeji:
وَزُرُوعٖ وَنَخۡلٖ طَلۡعُهَا هَضِيمٞ
"Da shuke-shuke da dabĩ nai, 'ya'yan itãcensu hirtsi* mãsu narkẽwa a ciki?"
* Hirtsi shi ne 'ya'yan itãce sãbabbi tun ba su nuna ba. Wãtau hirtsin gonakinsu idan an ci shi narkewã ya ke yi a cikin ciki, balle kuma 'ya'yan itãce nunannu.
Faccirooji aarabeeji:
وَتَنۡحِتُونَ مِنَ ٱلۡجِبَالِ بُيُوتٗا فَٰرِهِينَ
"Kuma kunã sassaƙa gidãje daga duwãtsu, kunã mãsu alfãhari?"
Faccirooji aarabeeji:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Faccirooji aarabeeji:
وَلَا تُطِيعُوٓاْ أَمۡرَ ٱلۡمُسۡرِفِينَ
"Kada ku yi ɗã'ã ga umurnin maɓarnata."
Faccirooji aarabeeji:
ٱلَّذِينَ يُفۡسِدُونَ فِي ٱلۡأَرۡضِ وَلَا يُصۡلِحُونَ
"Waɗanda suke yin ɓarna a cikin ƙasa, kuma bã su kyautatãwa."
Faccirooji aarabeeji:
قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلۡمُسَحَّرِينَ
Suka ce: "Kai daga mãsu sihiri kurum kake."
Faccirooji aarabeeji:
مَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا فَأۡتِ بِـَٔايَةٍ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّٰدِقِينَ
"Bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu. To, kã zo da wata ãyã idan kã kasance daga mãsu gaskiya."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ هَٰذِهِۦ نَاقَةٞ لَّهَا شِرۡبٞ وَلَكُمۡ شِرۡبُ يَوۡمٖ مَّعۡلُومٖ
Ya ce: "Wannan rãkuma ce tanã da shan* yini, kuma kunã da shan yini sasanne."
* Kuna zaton zã a bar ku a irin wannan ni'ima' Allah bã zai karɓi rãyukanku ba kuma Ya yi muku hisãbi a kanta? Kayya! Zã a yi muku hisãbi a bãyan kun mutu an tsayar da ku, dõmin hisãbin ayyukan da kuka yi.
Faccirooji aarabeeji:
وَلَا تَمَسُّوهَا بِسُوٓءٖ فَيَأۡخُذَكُمۡ عَذَابُ يَوۡمٍ عَظِيمٖ
"Kada ku shãfe ta da cũta har azãbar yini mai girmã ta shãfe ku."
Faccirooji aarabeeji:
فَعَقَرُوهَا فَأَصۡبَحُواْ نَٰدِمِينَ
Sai suka sõke ta sa'an nan suka wãyi gari sunã mãsu nadãma.
Faccirooji aarabeeji:
فَأَخَذَهُمُ ٱلۡعَذَابُۚ إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Sabõda haka azãba ta kãma su. Lalle ne a cikin wannan akwai ãyã, kuma mafi yawansu, ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Lalle ne Ubangijinka, haƙĩ ƙa, Shĩ ne Mabuwayi, Mai jin ƙai.
Faccirooji aarabeeji:
كَذَّبَتۡ قَوۡمُ لُوطٍ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Mutãnen Lũɗu sun ƙaryata Manzanni.
Faccirooji aarabeeji:
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ أَخُوهُمۡ لُوطٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da ɗan'uwansu,* Lũɗu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
* Lũɗu ɗan'uwansu ne na zaman gari da aure kawai. Asalinsa ɗan baffan Ibrãhĩm ne, sun tãso daga gabas, ƙasar Bãbila suka yi hijira, har ibrahĩm ya sauka Habrũna a ƙasar Shãm, Lũɗu kuwa ya sauka a sadũm da alƙaryunta.
Faccirooji aarabeeji:
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne nĩ, zuwa gare ku, Manzõ ne, amintacce."
Faccirooji aarabeeji:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa, kuma ku yi mini ɗã'ã."
Faccirooji aarabeeji:
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Kuma bã ni tambayar ku wata ijãra, Ijãrãta ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
Faccirooji aarabeeji:
أَتَأۡتُونَ ٱلذُّكۡرَانَ مِنَ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Shin kunã jẽ wa maza daga cikin talikai?"
Faccirooji aarabeeji:
وَتَذَرُونَ مَا خَلَقَ لَكُمۡ رَبُّكُم مِّنۡ أَزۡوَٰجِكُمۚ بَلۡ أَنتُمۡ قَوۡمٌ عَادُونَ
"Kuma kunã barin abin da Ubangijinku Ya halitta muku daga mãtanku? Ã'a, ku mutãne ne mãsu ƙẽtarẽwa!"
Faccirooji aarabeeji:
قَالُواْ لَئِن لَّمۡ تَنتَهِ يَٰلُوطُ لَتَكُونَنَّ مِنَ ٱلۡمُخۡرَجِينَ
Suka ce: "Lalle ne haƙĩƙa idan ba ka hanu ba, yã Lũɗu! Tĩlas ne kanã kasancẽwa daga waɗanda ake fitarwa (daga gari)."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ إِنِّي لِعَمَلِكُم مِّنَ ٱلۡقَالِينَ
Ya ce: "Lalle ne ga aikinku, haƙĩƙa, inã daga mãsu ƙinsa."
Faccirooji aarabeeji:
رَبِّ نَجِّنِي وَأَهۡلِي مِمَّا يَعۡمَلُونَ
"Ya Ubangijina! Ka tsĩrar da ni da iyãlĩna daga abin da suke aikatãwa."
Faccirooji aarabeeji:
فَنَجَّيۡنَٰهُ وَأَهۡلَهُۥٓ أَجۡمَعِينَ
Sabõda haka Muka tsĩrar da shi, Shi da mutãnensa gabã ɗaya.
Faccirooji aarabeeji:
إِلَّا عَجُوزٗا فِي ٱلۡغَٰبِرِينَ
Fãce wata tsõhuwa a cikin mãsu wanzuwa.
Faccirooji aarabeeji:
ثُمَّ دَمَّرۡنَا ٱلۡأٓخَرِينَ
Sa'an nan kuma Muka hallaka wasu. @Ko feewtinaa
Sa'an nan kuma Muka darkãke wasu.
Faccirooji aarabeeji:
وَأَمۡطَرۡنَا عَلَيۡهِم مَّطَرٗاۖ فَسَآءَ مَطَرُ ٱلۡمُنذَرِينَ
Kuma Muka yi ruwan sama a kansu ruwa, sai dai ruwan waɗanda ake yi wa gargaɗi ya mũnana.
Faccirooji aarabeeji:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle ne ga wannan, akwai ãyã, kuma mafi yawansu bã su kasance mãsu ĩmãni ba.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle ne Ubangijinka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Faccirooji aarabeeji:
كَذَّبَ أَصۡحَٰبُ لۡـَٔيۡكَةِ ٱلۡمُرۡسَلِينَ
Ma'abũta ƙunci sun ƙaryata Manzanni.
Faccirooji aarabeeji:
إِذۡ قَالَ لَهُمۡ شُعَيۡبٌ أَلَا تَتَّقُونَ
A lõkacin da Shu'aibu ya ce musu, "Bã zã ku yi taƙawa ba?"
Faccirooji aarabeeji:
إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
"Lalle ne ni, zuwa gare ku, Manzo ne, amintacce."
Faccirooji aarabeeji:
فَٱتَّقُواْ ٱللَّهَ وَأَطِيعُونِ
"Sabõda haka ku bi Allah da taƙawa kuma ku yi mini ɗã'ã."
Faccirooji aarabeeji:
وَمَآ أَسۡـَٔلُكُمۡ عَلَيۡهِ مِنۡ أَجۡرٍۖ إِنۡ أَجۡرِيَ إِلَّا عَلَىٰ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
"Kuma ba ni tambayar ku wata ijãra a kansa. Ijãrata ba ta zama ba fãce daga Ubangijin halittu."
Faccirooji aarabeeji:
۞ أَوۡفُواْ ٱلۡكَيۡلَ وَلَا تَكُونُواْ مِنَ ٱلۡمُخۡسِرِينَ
"Ku cika mũdu, kuma kada ku kasance daga mãsu sanyãwar hasãra (ga mutãne)."
Faccirooji aarabeeji:
وَزِنُواْ بِٱلۡقِسۡطَاسِ ٱلۡمُسۡتَقِيمِ
"Kuma ku yi awo da sikẽli daidaitacce."
Faccirooji aarabeeji:
وَلَا تَبۡخَسُواْ ٱلنَّاسَ أَشۡيَآءَهُمۡ وَلَا تَعۡثَوۡاْ فِي ٱلۡأَرۡضِ مُفۡسِدِينَ
"Kuma kada ku nakasa wa mutãne abũbuwansu kuma kada ku yi fasãdi a cikin ƙasa kuna mãsu ɓarna."
Faccirooji aarabeeji:
وَٱتَّقُواْ ٱلَّذِي خَلَقَكُمۡ وَٱلۡجِبِلَّةَ ٱلۡأَوَّلِينَ
"Kuma ku ji tsõron Allah wanda Ya halitta ku, kũ da jama'ar farko."
Faccirooji aarabeeji:
قَالُوٓاْ إِنَّمَآ أَنتَ مِنَ ٱلۡمُسَحَّرِينَ
Suka ce: "Kai dai daga waɗanda suke sihirtattu kawai ne."
Faccirooji aarabeeji:
وَمَآ أَنتَ إِلَّا بَشَرٞ مِّثۡلُنَا وَإِن نَّظُنُّكَ لَمِنَ ٱلۡكَٰذِبِينَ
"Kuma bã kõwa kake ba, fãce mutum kamarmu kuma lalle ne munã zaton ka, haƙĩƙa, daga maƙaryata."
Faccirooji aarabeeji:
فَأَسۡقِطۡ عَلَيۡنَا كِسَفٗا مِّنَ ٱلسَّمَآءِ إِن كُنتَ مِنَ ٱلصَّٰدِقِينَ
"To ka jẽfo wani ɓaɓɓake daga sama a kanmu, idan ka kasance daga mãsu gaskiya."
Faccirooji aarabeeji:
قَالَ رَبِّيٓ أَعۡلَمُ بِمَا تَعۡمَلُونَ
Ya ce: "Ubangijĩna ne Mafi sani ga abin da kuke aikatãwa."
Faccirooji aarabeeji:
فَكَذَّبُوهُ فَأَخَذَهُمۡ عَذَابُ يَوۡمِ ٱلظُّلَّةِۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَذَابَ يَوۡمٍ عَظِيمٍ
Sai suka ƙaiyatã shi, sabõda haka, azãbar rãnar girgije* ta kãma su. Lalle ne ita, tã kasance azãbar yini mai girma.
* An ruwaito cewa Allah Ya bũɗe musu ƙõfar Jahannama, zãfi ya hana su zama akõ'ina cikin gidãjensu, sa'an nan aka sanya girgije ya yi musu inuwa mai sanyi-sanyi har suka tãru a ciki, sa'an nan aka sanya girgijen ya kãma da wuta a kansu suka ƙõne kurmus kamar an gasa fãra. Suka kõma tõka kamar yadda suka nema daga Shu'aibu da a jefa musu ɓaɓɓake daga sama idan ya zama daga mãsu gaskiya.
Faccirooji aarabeeji:
إِنَّ فِي ذَٰلِكَ لَأٓيَةٗۖ وَمَا كَانَ أَكۡثَرُهُم مُّؤۡمِنِينَ
Lalle a cikin wancan haƙĩka akwai ãya, amma mafi yawansu ba su kasance mãsu ĩmãni ba.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّ رَبَّكَ لَهُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
Kuma lalle Ubangijĩnka, haƙĩƙa, Shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّهُۥ لَتَنزِيلُ رَبِّ ٱلۡعَٰلَمِينَ
Kuma lalle shi (Alƙur'ãni), haƙĩƙa, saukarwar Ubangijinhalittu ne.
Faccirooji aarabeeji:
نَزَلَ بِهِ ٱلرُّوحُ ٱلۡأَمِينُ
Rũhi* amintacce ne ya sauka da shi.
* Rũhul Ƙudus, shi ne Jibirĩl, amincin Allah ya tabbata a gare shi.
Faccirooji aarabeeji:
عَلَىٰ قَلۡبِكَ لِتَكُونَ مِنَ ٱلۡمُنذِرِينَ
A kan zũciyarka, dõmin ka kasance daga mãsu gargaɗi.
Faccirooji aarabeeji:
بِلِسَانٍ عَرَبِيّٖ مُّبِينٖ
Da harshe na Larabci mai bayãni.
Faccirooji aarabeeji:
وَإِنَّهُۥ لَفِي زُبُرِ ٱلۡأَوَّلِينَ
Kuma lalle shin, haƙĩƙa, yanã a cikin litattafan (Manzannin) farko.
Faccirooji aarabeeji:
أَوَلَمۡ يَكُن لَّهُمۡ ءَايَةً أَن يَعۡلَمَهُۥ عُلَمَٰٓؤُاْ بَنِيٓ إِسۡرَٰٓءِيلَ
Ashe, bai kasance ãyã ba a gare su, ya zama Mãlaman Banĩ Isrã'ĩla sun san shi?
Faccirooji aarabeeji:
وَلَوۡ نَزَّلۡنَٰهُ عَلَىٰ بَعۡضِ ٱلۡأَعۡجَمِينَ
Kuma dã mun saukar da shi a kan sãshen Ajamãwa,
Faccirooji aarabeeji:
فَقَرَأَهُۥ عَلَيۡهِم مَّا كَانُواْ بِهِۦ مُؤۡمِنِينَ
Ya karanta shi a kansu, ba su kasance sabõda shi mãsu ĩmãni ba.
Faccirooji aarabeeji:
كَذَٰلِكَ سَلَكۡنَٰهُ فِي قُلُوبِ ٱلۡمُجۡرِمِينَ
Kamar wancan ne! Muka shigar da shi a cikin zukãtan mãsu laifi.
Faccirooji aarabeeji:
لَا يُؤۡمِنُونَ بِهِۦ حَتَّىٰ يَرَوُاْ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَلِيمَ
Bã zã su yi ĩmãni da shĩ ba sai sun ga azãbar nan mai raɗadi.
Faccirooji aarabeeji:
فَيَأۡتِيَهُم بَغۡتَةٗ وَهُمۡ لَا يَشۡعُرُونَ
Sai ta taho musu kwatsam, alhãli kuwa sũ, ba su sansance ba.
Faccirooji aarabeeji:
فَيَقُولُواْ هَلۡ نَحۡنُ مُنظَرُونَ
Sai su ce: "Shin, mu waɗanda ake yi wa jinkiri ne?"
Faccirooji aarabeeji:
أَفَبِعَذَابِنَا يَسۡتَعۡجِلُونَ
Ashe, to, da azãbar Mu suke nẽman gaggãwa?
Faccirooji aarabeeji:
أَفَرَءَيۡتَ إِن مَّتَّعۡنَٰهُمۡ سِنِينَ
Ashe, to, kã gani, idan Muka jĩshe su daɗi a shẽkaru,
Faccirooji aarabeeji:
ثُمَّ جَآءَهُم مَّا كَانُواْ يُوعَدُونَ
Sa'an nan abin da suka kasance anã yi musu wa'adi (da shi) ya jẽ musu,
Faccirooji aarabeeji:
مَآ أَغۡنَىٰ عَنۡهُم مَّا كَانُواْ يُمَتَّعُونَ
Abin da suka kasance anã jĩshe su dãɗin bã zai tunkuɗe azãba ba daga gare* su.
* Dã an bã su lõkaci mai tsawo sunã jin dãɗi da rãyuwar dũniya a cikinsa, to, rãnar da mutuwa kõ azãbar Allah ta je gare su, wannan lõkacin bã zai tunkuɗe mutuwar kõ azabar ba daga gare su.
Faccirooji aarabeeji:
وَمَآ أَهۡلَكۡنَا مِن قَرۡيَةٍ إِلَّا لَهَا مُنذِرُونَ
Kuma bã Mu halakar da wata alƙarya ba fãce tanã da mãsu gargaɗi.
Faccirooji aarabeeji:
ذِكۡرَىٰ وَمَا كُنَّا ظَٰلِمِينَ
Dõmin tunãtarwa, kuma ba Mu kasance Mãsu zãlunci ba.
Faccirooji aarabeeji:
وَمَا تَنَزَّلَتۡ بِهِ ٱلشَّيَٰطِينُ
Kuma (Alƙur'ãni) Shaiɗãnu ba su ɗõra sauka da shĩba.
Faccirooji aarabeeji:
وَمَا يَنۢبَغِي لَهُمۡ وَمَا يَسۡتَطِيعُونَ
Kuma bã ya kamãta a gare su (su Shaiɗãnu su sauka da shi), kuma ba su iyãwa.
Faccirooji aarabeeji:
إِنَّهُمۡ عَنِ ٱلسَّمۡعِ لَمَعۡزُولُونَ
Lalle ne sũ, daga saurãre, haƙĩƙa, waɗanda aka nĩsantar ne.
Faccirooji aarabeeji:
فَلَا تَدۡعُ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَ فَتَكُونَ مِنَ ٱلۡمُعَذَّبِينَ
Sabõda haka, kada ka kira wani abin bautãwa na dabam tãre da Allah, sai ka kasance daga waɗanda ake yi wa azãba.
Faccirooji aarabeeji:
وَأَنذِرۡ عَشِيرَتَكَ ٱلۡأَقۡرَبِينَ
Kuma ka yi gargaɗi ga danginka mafiya kusanci.
Faccirooji aarabeeji:
وَٱخۡفِضۡ جَنَاحَكَ لِمَنِ ٱتَّبَعَكَ مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Kuma ka sassauta fikãfikanka* ga wanda ya bĩ ka daga mũminai.
* Ka zama mai tausayi ga mũminai waɗanda suka bĩ ka, ka yi musu kamar yadda kãzã take yi wa 'ya'yanta ƙanana a lõkacin sanyi, kõ kuwa idan zã su yi barci dõmin ta kãre su daga cũta.
Faccirooji aarabeeji:
فَإِنۡ عَصَوۡكَ فَقُلۡ إِنِّي بَرِيٓءٞ مِّمَّا تَعۡمَلُونَ
Sa'an nan idan suka sãɓã maka to ka ce: "Lalle nĩ, barrantacce ne daga abin da kuko aikatãwa."
Faccirooji aarabeeji:
وَتَوَكَّلۡ عَلَى ٱلۡعَزِيزِ ٱلرَّحِيمِ
Kuma ka dõgara ga Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Faccirooji aarabeeji:
ٱلَّذِي يَرَىٰكَ حِينَ تَقُومُ
Wanda Yake ganin ka a lõkacin da kake tãshi tsaye.
Faccirooji aarabeeji:
وَتَقَلُّبَكَ فِي ٱلسَّٰجِدِينَ
Da jujjuyãwarka a cikin mãsu yin sujada.
Faccirooji aarabeeji:
إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ
Lalle Shi, Shi* ne Mai ji, Masani.
* Allah Shi ne Mai ji, ji na gaskiya, kuma Masani, sani na gaskiya.
Faccirooji aarabeeji:
هَلۡ أُنَبِّئُكُمۡ عَلَىٰ مَن تَنَزَّلُ ٱلشَّيَٰطِينُ
Shin, (kunã so) in gaya* muku a kan wanda Shaiɗãnnu kan sauka?
* Wannan dõmin raddi ne gamãsu cewa aljannu ke gayawa Muhammadu, tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, Alƙur'ãni. Aljannu bã su saukã sai ga maƙaryaci, mai zunubi' Muhammadu kuwa bã haka yake ba. Sabõda haka shi bã mahaukaci ba, kuma ba wanda aljannu suke gaya wa ba. Dukan abin da ya faɗa, to, wahayi ne daga Allah.
Faccirooji aarabeeji:
تَنَزَّلُ عَلَىٰ كُلِّ أَفَّاكٍ أَثِيمٖ
Sukan sauka a kan dukkan maƙaryaci, mai zunubi.
Faccirooji aarabeeji:
يُلۡقُونَ ٱلسَّمۡعَ وَأَكۡثَرُهُمۡ كَٰذِبُونَ
Sunã jẽfa (abin da suka) ji, alhãli kuwa mafi yawansu maƙaryata ne.
Faccirooji aarabeeji:
وَٱلشُّعَرَآءُ يَتَّبِعُهُمُ ٱلۡغَاوُۥنَ
Kuma mawãƙa* halakakku ne ke bin su.
* Siffõfin mawãƙa sun nũna cewa Annabi Muhammadu bã mawãƙi ba ne, dõmin bã shi da ɗaya daga cikin siffõfin mawãƙa. Kuma mabiyansa ba halakakku ba ne.
Faccirooji aarabeeji:
أَلَمۡ تَرَ أَنَّهُمۡ فِي كُلِّ وَادٖ يَهِيمُونَ
Shin, ba ku cẽwa, lalle ne sũ, cikin kõwane rango sunã yin ɗimuwa (su ƙẽtare haddi) ba?
Faccirooji aarabeeji:
وَأَنَّهُمۡ يَقُولُونَ مَا لَا يَفۡعَلُونَ
Kuma lalle ne, sũ, sunã faɗin abin da bã su aikatãwa?
Faccirooji aarabeeji:
إِلَّا ٱلَّذِينَ ءَامَنُواْ وَعَمِلُواْ ٱلصَّٰلِحَٰتِ وَذَكَرُواْ ٱللَّهَ كَثِيرٗا وَٱنتَصَرُواْ مِنۢ بَعۡدِ مَا ظُلِمُواْۗ وَسَيَعۡلَمُ ٱلَّذِينَ ظَلَمُوٓاْ أَيَّ مُنقَلَبٖ يَنقَلِبُونَ
Fãce waɗanda suka yi ĩmãni suka aikata ayyukan ƙwarai, kuma suka ambaci Allah da yawa, kuma suka rãma zãlunci, daga bãyan an zãlunce su. Kuma waɗanda suka yi zãlunci, zã su sani a wace majũya suke jũyãwa.
Faccirooji aarabeeji:
 
Firo maanaaji Simoore: Simoore yimooɓe
Tippudi cimooje Tonngoode hello ngoo
 
Firo maanaaji al-quraan tedduɗo oo - Firo hawsiiwo, Abuubakri Juumiy - Tippudi firooji ɗii

Firo maanaaji al-quraan tedduɗo oo e ɗemngal hawseer, firi ɗum ko Abuubakri Ngo feewnitaama e ngardiingo hentorde kanngameeji firo, ina newnaa ƴellitaade e firo asliiwo ngoo ngam feññinde yiyannde e horde e ƴellito duumiingo.

Uddude