Ibisobanuro bya qoran ntagatifu - Ibisobanuro mu gihawusawiya - abubakar djumiy * - Ishakiro ry'ibisobanuro

XML CSV Excel API
Please review the Terms and Policies

Ibisobanuro by'amagambo Isura: Dukhanu (Umwotsi)   Umurongo:

Suratu Al'dukhan

حمٓ
Ḥ. M̃.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَٱلۡكِتَٰبِ ٱلۡمُبِينِ
Inã rantsuwa da Littãfi Mabayyani.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّآ أَنزَلۡنَٰهُ فِي لَيۡلَةٖ مُّبَٰرَكَةٍۚ إِنَّا كُنَّا مُنذِرِينَ
Lalle ne, Mũ, Muka saukar da shi a cikin wani dare mai albarka. Lalle Mũ' Mun kasance Mãsu yin gargaɗi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فِيهَا يُفۡرَقُ كُلُّ أَمۡرٍ حَكِيمٍ
A cikinsa (shi daren) ake rarrabe kõwane umurui bayyananne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَمۡرٗا مِّنۡ عِندِنَآۚ إِنَّا كُنَّا مُرۡسِلِينَ
Umurni na daga wurin Mu. Lalle Mũ ne Muka kasance Mãsu aikãwã.
Ibisobanuro by'icyarabu:
رَحۡمَةٗ مِّن رَّبِّكَۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلسَّمِيعُ ٱلۡعَلِيمُ
Sabõda rahama daga Ubangijinka. Lalle Shĩ, Shi ne Mai ji, Mãsani.
Ibisobanuro by'icyarabu:
رَبِّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضِ وَمَا بَيۡنَهُمَآۖ إِن كُنتُم مُّوقِنِينَ
(Shĩ ne) Ubangijin sammai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu, idan kun kasance mãsu yaƙĩni (za ku gãne haka).
Ibisobanuro by'icyarabu:
لَآ إِلَٰهَ إِلَّا هُوَ يُحۡيِۦ وَيُمِيتُۖ رَبُّكُمۡ وَرَبُّ ءَابَآئِكُمُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Babu abin bautãwa fãce Shi. Yana rãyarwa Kuma Yana kashẽwa. (Shi ne) Ubangijinku, kuma Ubangijin ubanninku na farko.
Ibisobanuro by'icyarabu:
بَلۡ هُمۡ فِي شَكّٖ يَلۡعَبُونَ
A'a sũ, sunã wãsã a cikin shakka.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱرۡتَقِبۡ يَوۡمَ تَأۡتِي ٱلسَّمَآءُ بِدُخَانٖ مُّبِينٖ
Sabõda haka, ka dakata rãnar da sama zã tã zo da hayãƙi bayyananne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
يَغۡشَى ٱلنَّاسَۖ هَٰذَا عَذَابٌ أَلِيمٞ
Yanã rufe mutãne. Wannan wata azãba ce mai raɗaɗi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
رَّبَّنَا ٱكۡشِفۡ عَنَّا ٱلۡعَذَابَ إِنَّا مُؤۡمِنُونَ
Ya Ubangijinmu! Ka kuranye mana azãba. Lalle Mũ, mãsu ĩmãni ne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَنَّىٰ لَهُمُ ٱلذِّكۡرَىٰ وَقَدۡ جَآءَهُمۡ رَسُولٞ مُّبِينٞ
Inã tunãwa take a gare su, alhãli kuwa, haƙĩƙa, Manzo mai bayyanãwa Ya je musu (da gargaɗin saukar azãbar, ba su karɓa ba)?
Ibisobanuro by'icyarabu:
ثُمَّ تَوَلَّوۡاْ عَنۡهُ وَقَالُواْ مُعَلَّمٞ مَّجۡنُونٌ
Sa'an nan suka jũya baya daga gare shi, Kuma suka ce: "Wanda ake gayãwa* ne, mahaukaci."
* Sunã nufin waɗansu mutãne ne ke gaya wa Annabi Alƙur'ãni, kõ kuma daga alãma watau wai Annabi taɓaɓɓe ne, mahaukaci. Taɓaɓɓe da mahaukaci duka ma'anarsu guda ce, watau marashin hankali,wanda aka yi wa alãma da rashin hankali.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّا كَاشِفُواْ ٱلۡعَذَابِ قَلِيلًاۚ إِنَّكُمۡ عَآئِدُونَ
Lalle Mũ, Mãsu kuranyẽwar azãba ne, a ɗan lõkaci kaɗan, lalle kũ, mãsu kõmãwa ne (ga laifin).
Ibisobanuro by'icyarabu:
يَوۡمَ نَبۡطِشُ ٱلۡبَطۡشَةَ ٱلۡكُبۡرَىٰٓ إِنَّا مُنتَقِمُونَ
Rãnar da Muke damƙa, damƙa mafi girma, lalle ne Mũ mãsu azãbar rãmuwa ne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
۞ وَلَقَدۡ فَتَنَّا قَبۡلَهُمۡ قَوۡمَ فِرۡعَوۡنَ وَجَآءَهُمۡ رَسُولٞ كَرِيمٌ
Kuma lalle ne haƙĩƙa a gabaninsu, Mun fitini mutãnen Fir'auna, kuma wani Manzo karĩmi ya jẽ musu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَنۡ أَدُّوٓاْ إِلَيَّ عِبَادَ ٱللَّهِۖ إِنِّي لَكُمۡ رَسُولٌ أَمِينٞ
(Mazon ya ce): "Ku kãwo mini (ĩmãninku) ya bayin Allah! Lalle ni, Manzo ne amintacce zuwa gare ku."
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَأَن لَّا تَعۡلُواْ عَلَى ٱللَّهِۖ إِنِّيٓ ءَاتِيكُم بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٖ
"Kuma kada ku nẽmi ɗaukaka a kan Allah. Lalle nĩ mai zo muku ne da dalĩli bayyananne."
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِنِّي عُذۡتُ بِرَبِّي وَرَبِّكُمۡ أَن تَرۡجُمُونِ
"Kuma lalle nĩ na nẽmi tsari da Ubangijĩna, kuma Ubangijinku, dõmin kada ku jẽfe ni."
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِن لَّمۡ تُؤۡمِنُواْ لِي فَٱعۡتَزِلُونِ
"Kuma idan ba ku yi ĩmãni sabõda nĩ ba, to, ku nĩsance ni."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَدَعَا رَبَّهُۥٓ أَنَّ هَٰٓؤُلَآءِ قَوۡمٞ مُّجۡرِمُونَ
Sai ya kirayi Ubangjinsa cẽwa waɗannan mutãnene mãsu laifi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأَسۡرِ بِعِبَادِي لَيۡلًا إِنَّكُم مُّتَّبَعُونَ
(Allah Ya ce): "To, ka yi tafiyar dare da bayiNa, da dare. Lalle kũ, waɗanda ake bĩ ne (dõmin a kãma ku.)"
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَٱتۡرُكِ ٱلۡبَحۡرَ رَهۡوًاۖ إِنَّهُمۡ جُندٞ مُّغۡرَقُونَ
"Kuma ka bar tẽku rarrabe. Lalle sũ, runduna ce abar nutsarwa."
Ibisobanuro by'icyarabu:
كَمۡ تَرَكُواْ مِن جَنَّٰتٖ وَعُيُونٖ
Da yawa suka bar gõnaki da marẽmari.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَزُرُوعٖ وَمَقَامٖ كَرِيمٖ
Da shuke-shuke da matsayi mai kyau.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَنَعۡمَةٖ كَانُواْ فِيهَا فَٰكِهِينَ
Da wata ni'ima da suka kasance a cikinta sunã mãsu hutu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
كَذَٰلِكَۖ وَأَوۡرَثۡنَٰهَا قَوۡمًا ءَاخَرِينَ
Kamar haka! Kuma Muka gãdar da ita ga waɗansu mutãne na dabam.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَمَا بَكَتۡ عَلَيۡهِمُ ٱلسَّمَآءُ وَٱلۡأَرۡضُ وَمَا كَانُواْ مُنظَرِينَ
Sa'an nan samã da ƙasã ba su yi kũka *a kansu ba, Kuma ba su kasance waɗanda ake yi wa jinkiri ba.
* Watau sama da ƙasa ba su girgizu ba sabõda halaka su da aka yi kamar ba a yi, kõme ba.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَلَقَدۡ نَجَّيۡنَا بَنِيٓ إِسۡرَٰٓءِيلَ مِنَ ٱلۡعَذَابِ ٱلۡمُهِينِ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa Mun tsĩrar da Banĩ Isrã'ĩla daga, azãba mai wulãkantãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
مِن فِرۡعَوۡنَۚ إِنَّهُۥ كَانَ عَالِيٗا مِّنَ ٱلۡمُسۡرِفِينَ
Daga Fir'auna. Lalle shi, ya kasance maɗaukaki daga cikin mãsu ɓarna.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَلَقَدِ ٱخۡتَرۡنَٰهُمۡ عَلَىٰ عِلۡمٍ عَلَى ٱلۡعَٰلَمِينَ
Kuma lalle ne, haƙĩƙa, Mun zãɓe su sabõda wani ilmi (na Taurata) a kan mutãne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَءَاتَيۡنَٰهُم مِّنَ ٱلۡأٓيَٰتِ مَا فِيهِ بَلَٰٓؤٞاْ مُّبِينٌ
Kuma Muka bã su, daga ãyõyin mu'ujizõji, abin da yake a cikinsa, akwai ni'ima bayyananna*
* An bai wa Banĩ lsrã'ĩla ni'imar ilmi na Taurãta, an ɗaukaka su, sabõda aiki da ilmin, a kan sauran mutãnen zãmaninsu, kuma aka bã su ãyõyin mu'ujiza kamar tsãge teku da mannu da salwa da sauransu, amma kuma dukkan waɗannan ni'imomĩn sai da suka gushe a lõkacin da suka sãɓawa umurnin Allah, sai kuma ƙasƙanci ya maye musu daga bãya. Wannan kuma wa'azi ne ga Musulmi waɗanda Allah Ya ɗaukaka su da Alƙur'ãni a kan sauran mutãne, idan sun kauce masa zã su wulãkantu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّ هَٰٓؤُلَآءِ لَيَقُولُونَ
Lalle waɗannan mutãne*, haƙĩka, sunã cẽwa,
* Anã nufin mutãnen zãmanin Annabi Muhammadu, tsĩra da aminci su tabbata a gare shi, waɗanda ake kiran su zuwa ga Musulunci.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنۡ هِيَ إِلَّا مَوۡتَتُنَا ٱلۡأُولَىٰ وَمَا نَحۡنُ بِمُنشَرِينَ
"Babu wani abu sai mutuwarmu ta farko, kuma ba mu zama waɗanda ake tãyarwa ba."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأۡتُواْ بِـَٔابَآئِنَآ إِن كُنتُمۡ صَٰدِقِينَ
"Sai ku zo da ubanninmu, idan kun kasance mãsu gaskiya."
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَهُمۡ خَيۡرٌ أَمۡ قَوۡمُ تُبَّعٖ وَٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِمۡ أَهۡلَكۡنَٰهُمۡۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ مُجۡرِمِينَ
shin, sũ ne mafĩfĩta kõ kuwa mutãnen Tubba'u, kuma da waɗanda ke a gabãninsu? Mun halaka su, lalle sũ, sun kasance mãsu laifi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَمَا خَلَقۡنَا ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلۡأَرۡضَ وَمَا بَيۡنَهُمَا لَٰعِبِينَ
Kuma ba Mu halitta slmmai da ƙasa da abin da ke a tsakãninsu ba, alhãli kuwa Munã mãsu wãsã.
Ibisobanuro by'icyarabu:
مَا خَلَقۡنَٰهُمَآ إِلَّا بِٱلۡحَقِّ وَلَٰكِنَّ أَكۡثَرَهُمۡ لَا يَعۡلَمُونَ
Ba Mu halitta su ba fãce da manufa ta gaskiya, kuma amma mafi yawansu, ba su sani ba.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّ يَوۡمَ ٱلۡفَصۡلِ مِيقَٰتُهُمۡ أَجۡمَعِينَ
Lalle rãnar rarrabẽwa, ita ce lõkacin wa'adinsu gabã ɗaya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
يَوۡمَ لَا يُغۡنِي مَوۡلًى عَن مَّوۡلٗى شَيۡـٔٗا وَلَا هُمۡ يُنصَرُونَ
Rãnar da wani zumu bã ya amfãnin wani zumu da kõme kuma ba su zama anã taimakon su ba.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِلَّا مَن رَّحِمَ ٱللَّهُۚ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلرَّحِيمُ
fãce wanda Allah Ya yi wa rahama. Lalle Shi (Allah), shĩ ne Mabuwãyi, Mai jin ƙai.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّ شَجَرَتَ ٱلزَّقُّومِ
Lalle itãciyar zaƙƙũm (ɗanyen wutã),
Ibisobanuro by'icyarabu:
طَعَامُ ٱلۡأَثِيمِ
Ita ce abincin mai laifi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
كَٱلۡمُهۡلِ يَغۡلِي فِي ٱلۡبُطُونِ
Kamar narkakken kwalta yanã tafasa a cikin cikunna.
Ibisobanuro by'icyarabu:
كَغَلۡيِ ٱلۡحَمِيمِ
Kamar tafasar ruwan zãfi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
خُذُوهُ فَٱعۡتِلُوهُ إِلَىٰ سَوَآءِ ٱلۡجَحِيمِ
(A cẽ wa malã'ikun wutã), "Ku kãmã shi, sa'an nan ku fizge shi zuwa ga tsakiyar Jahĩm."
Ibisobanuro by'icyarabu:
ثُمَّ صُبُّواْ فَوۡقَ رَأۡسِهِۦ مِنۡ عَذَابِ ٱلۡحَمِيمِ
"Sa'an nan ku zuba, a kansa, daga azãbar ruwan zãfi."
Ibisobanuro by'icyarabu:
ذُقۡ إِنَّكَ أَنتَ ٱلۡعَزِيزُ ٱلۡكَرِيمُ
(A ce masã), "Ka ɗanɗana! Lalle kai, kai ne mabuwãyi mai girma!"
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّ هَٰذَا مَا كُنتُم بِهِۦ تَمۡتَرُونَ
"Lalle wannan, shi ne abin da kuka kasance kunã shakka game da shi."
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي مَقَامٍ أَمِينٖ
Lalle mãsu taƙawa sunã cikin matsayi amintacce.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فِي جَنَّٰتٖ وَعُيُونٖ
A cikin gidãjen Aljanna da marẽmari.
Ibisobanuro by'icyarabu:
يَلۡبَسُونَ مِن سُندُسٖ وَإِسۡتَبۡرَقٖ مُّتَقَٰبِلِينَ
Sunã tufanta daga tufãfin alharĩni raƙĩƙi, da mai kauri, sunã mãsu zaman fuskantar jũna.
Ibisobanuro by'icyarabu:
كَذَٰلِكَ وَزَوَّجۡنَٰهُم بِحُورٍ عِينٖ
Kamar haka, kuma Mun aurar da su da mãtã mãsu kyawun idãnu, mãsu girmansu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
يَدۡعُونَ فِيهَا بِكُلِّ فَٰكِهَةٍ ءَامِنِينَ
Sunã kira, a cikinsu (gidẽjen) ga dukan 'ya'yan itãcen marmari, sunã amintattu (daga dukan abin tsõro).
Ibisobanuro by'icyarabu:
لَا يَذُوقُونَ فِيهَا ٱلۡمَوۡتَ إِلَّا ٱلۡمَوۡتَةَ ٱلۡأُولَىٰۖ وَوَقَىٰهُمۡ عَذَابَ ٱلۡجَحِيمِ
Bã su ɗanɗanar mutuwa, a cikinsu, fãce mutuwar farko, kuma (Allah), Ya tsare musu azãbar Jahĩm.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَضۡلٗا مِّن رَّبِّكَۚ ذَٰلِكَ هُوَ ٱلۡفَوۡزُ ٱلۡعَظِيمُ
Sabõda falala daga Ubangijinka. Wancan shi ne babban rabo, mai girma.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَإِنَّمَا يَسَّرۡنَٰهُ بِلِسَانِكَ لَعَلَّهُمۡ يَتَذَكَّرُونَ
Dõmin haka kawai Muka sauƙaƙar da shi (Alƙur'ãni) da harshenka, tsammãninsu, su riƙa tunãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱرۡتَقِبۡ إِنَّهُم مُّرۡتَقِبُونَ
Sai ka yi jira. Lalle sũ, mãsu jira ne.*
* Mãsu jira ne ga abin da zai sãme su idan ba su yi ĩmãni ba, watau ni'imar da aka ba su zã ta gushe ke nan dõmin ba su aiwatar da ita ba a kan umuruin Allah.
Ibisobanuro by'icyarabu:
 
Ibisobanuro by'amagambo Isura: Dukhanu (Umwotsi)
Urutonde rw'amasura numero y'urupapuro
 
Ibisobanuro bya qoran ntagatifu - Ibisobanuro mu gihawusawiya - abubakar djumiy - Ishakiro ry'ibisobanuro

ibisobanuro bya Qoraan ntagatifu mururimi rw'igihawusa byasobanuwe na Abuubakri Muhamudi Juumi byakosowe kd bihagararirwa nikigo rawaad tarjamat hagamijwe kugera kubisonuro byumwimerere no kungurana ibitekerezo niterambere rirambye

Gufunga