Ibisobanuro bya qoran ntagatifu - Ibisobanuro mu gihawusawiya - abubakar djumiy * - Ishakiro ry'ibisobanuro

XML CSV Excel API
Please review the Terms and Policies

Ibisobanuro by'amagambo Isura: Alqalam (Ikaramu)   Umurongo:

Suratu Al'kalam

نٓۚ وَٱلۡقَلَمِ وَمَا يَسۡطُرُونَ
Ñ. Na rantse da alƙalami da abin da (marubũta) suke rubũtãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
مَآ أَنتَ بِنِعۡمَةِ رَبِّكَ بِمَجۡنُونٖ
Kai, sabõda ni'imar Ubangijinka, bã mahaukaci kake ba.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِنَّ لَكَ لَأَجۡرًا غَيۡرَ مَمۡنُونٖ
Kuma, lalle, haƙĩƙa kanã da lãdar da bã ta yankewa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِنَّكَ لَعَلَىٰ خُلُقٍ عَظِيمٖ
Kuma, lalle haƙiƙa kana a kan hãlãyen kirki, manya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَسَتُبۡصِرُ وَيُبۡصِرُونَ
Don haka, zã ka gani, sũ kuma zã su gani.
Ibisobanuro by'icyarabu:
بِأَييِّكُمُ ٱلۡمَفۡتُونُ
Ga wanenku haukã take.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّ رَبَّكَ هُوَ أَعۡلَمُ بِمَن ضَلَّ عَن سَبِيلِهِۦ وَهُوَ أَعۡلَمُ بِٱلۡمُهۡتَدِينَ
Lalle Ubangijinka Shi ne Mafi sani ga wanda ya ɓace daga tafarkin Sa. Kuma Shi ne Mafi sani ga mãsu shiryuwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَلَا تُطِعِ ٱلۡمُكَذِّبِينَ
Saboda haka kada ka bi mãsu ƙaryatãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَدُّواْ لَوۡ تُدۡهِنُ فَيُدۡهِنُونَ
Sunã fatar ka sassauta, su kuma sũ sassauta.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَلَا تُطِعۡ كُلَّ حَلَّافٖ مَّهِينٍ
Kada ka bi dukkan mai yawan rantsuwa, walãkantacce.
Ibisobanuro by'icyarabu:
هَمَّازٖ مَّشَّآءِۭ بِنَمِيمٖ
Mai zunɗe, mai yãwo da gulma.
Ibisobanuro by'icyarabu:
مَّنَّاعٖ لِّلۡخَيۡرِ مُعۡتَدٍ أَثِيمٍ
Mai hana alhẽri mai zãlunci, mai zunubi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
عُتُلِّۭ بَعۡدَ ذَٰلِكَ زَنِيمٍ
Mai girman kai, bãyan haka kuma la'ĩmi (bã ya son alhẽri).
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَن كَانَ ذَا مَالٖ وَبَنِينَ
Sabõda yã kasance mai dũkiya da ɗiya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِذَا تُتۡلَىٰ عَلَيۡهِ ءَايَٰتُنَا قَالَ أَسَٰطِيرُ ٱلۡأَوَّلِينَ
Idan ana karanta masa ãyõyin Mu, sai ya ce: "Tatsũniyõyin mutãnen farko ne."
Ibisobanuro by'icyarabu:
سَنَسِمُهُۥ عَلَى ٱلۡخُرۡطُومِ
Zã Mu yi masa alãma a kan hanci.
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّا بَلَوۡنَٰهُمۡ كَمَا بَلَوۡنَآ أَصۡحَٰبَ ٱلۡجَنَّةِ إِذۡ أَقۡسَمُواْ لَيَصۡرِمُنَّهَا مُصۡبِحِينَ
Lalle Mun jarrabe su kamar yadda Muka jarrabi mãsu gonar lambu, a lokacin da suka yi rantsuwa, wai lalle zã su girbe amfãninta, suna mãsu asubanci.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَلَا يَسۡتَثۡنُونَ
Kuma (suka yi niyya), bã su kõ tõgẽwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَطَافَ عَلَيۡهَا طَآئِفٞ مِّن رَّبِّكَ وَهُمۡ نَآئِمُونَ
Wani mai kẽwayãwa daga Ubangijinka ya kẽwayã a kanta, (ya ƙone ta,) alhãli sunã barci.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأَصۡبَحَتۡ كَٱلصَّرِيمِ
Sai ta wãyi gari (baƙa ƙirin) kamar dare.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَتَنَادَوۡاْ مُصۡبِحِينَ
Sai suka kirãyi jũna, sunã mãsu yin asubanci.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَنِ ٱغۡدُواْ عَلَىٰ حَرۡثِكُمۡ إِن كُنتُمۡ صَٰرِمِينَ
Cẽwa ku yi sammakõ ga amfãnin gõnarku, idan kun kasance mãsu girbewa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱنطَلَقُواْ وَهُمۡ يَتَخَٰفَتُونَ
Sai suka tafi sunã shãwara a ɓõye (sunã cẽwa).
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَن لَّا يَدۡخُلَنَّهَا ٱلۡيَوۡمَ عَلَيۡكُم مِّسۡكِينٞ
"Lalle kada wani miskĩni ya shigar muku ita a yau!"
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَغَدَوۡاْ عَلَىٰ حَرۡدٖ قَٰدِرِينَ
Kuma suka yi sammako akan (niyyar) rõwa, matuƙar iyãwarsu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَلَمَّا رَأَوۡهَا قَالُوٓاْ إِنَّا لَضَآلُّونَ
Lõkacin da suka gan ta, sai suka ce: "Lalle, mun saki hanya (mun ɓace)!"
Ibisobanuro by'icyarabu:
بَلۡ نَحۡنُ مَحۡرُومُونَ
"Ba haka ba, mũ dai, an hana mu ne."
Ibisobanuro by'icyarabu:
قَالَ أَوۡسَطُهُمۡ أَلَمۡ أَقُل لَّكُمۡ لَوۡلَا تُسَبِّحُونَ
Mafificinsu (hankali) ya ce: "Ban gaya muku ba, yã kamata ku tsarkake Allah?"
Ibisobanuro by'icyarabu:
قَالُواْ سُبۡحَٰنَ رَبِّنَآ إِنَّا كُنَّا ظَٰلِمِينَ
Suka ce: "Tsarki ya tabbata ga Ubangijinmu! Lalle, mu mun kasance azzãlumai."
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأَقۡبَلَ بَعۡضُهُمۡ عَلَىٰ بَعۡضٖ يَتَلَٰوَمُونَ
Sai suka fuskanci jũna, sunã zargin kansu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
قَالُواْ يَٰوَيۡلَنَآ إِنَّا كُنَّا طَٰغِينَ
Suka ce: "Kaitonmu! Lalle, mũ ne muka kasance mãsu ƙẽtare iyãka."
Ibisobanuro by'icyarabu:
عَسَىٰ رَبُّنَآ أَن يُبۡدِلَنَا خَيۡرٗا مِّنۡهَآ إِنَّآ إِلَىٰ رَبِّنَا رَٰغِبُونَ
"Mai yiwuwa ne Ubangijinmu Ya musanya mana da wani abu da yã fi ta. Lalle, mũ (ba mu yanke ƙauna ba) zuwa ga Ubangijinmu, mãsu kwaɗayi ne."
Ibisobanuro by'icyarabu:
كَذَٰلِكَ ٱلۡعَذَابُۖ وَلَعَذَابُ ٱلۡأٓخِرَةِ أَكۡبَرُۚ لَوۡ كَانُواْ يَعۡلَمُونَ
Haka dai azãbar* take, kuma lalle ne azãbar Lãhira ta fi girma, in da sun kasance zã su iya gãnẽwã.
* Irin wannan azãba ce za a yi wa Ƙuraishãwa, dangin Annabi, kamar yadda aka yi wa mãsu gonar lambu, wãto da suka tũba aka musanya musu da abin da ya fi abin da suka sãba sãmu. Wato an gayã wa Annabi ne lõkacin da danginsa suka kangare, suka ƙi shiga Musulunci, aka yi musu azãbar fari, da rashin ruwa shekara bakwai, Allah Ya gaya masa cewa, zã su musulunta, alheri ya kõma musu. Ya kuwa kõma, kamar yadda Allah Ya yi alkawari
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّ لِلۡمُتَّقِينَ عِندَ رَبِّهِمۡ جَنَّٰتِ ٱلنَّعِيمِ
Lalle ne mãsu taƙawa nã da a wurin Ubangijinsu, gidãjen Aljanna na ni'ima.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَفَنَجۡعَلُ ٱلۡمُسۡلِمِينَ كَٱلۡمُجۡرِمِينَ
Shin ko zã Mu sanya waɗanda ke bi da ɗa'a kamar mãsu laifi?
Ibisobanuro by'icyarabu:
مَا لَكُمۡ كَيۡفَ تَحۡكُمُونَ
Me ya sãme ku, yãya kuke yin hukunci (da haka)?
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَمۡ لَكُمۡ كِتَٰبٞ فِيهِ تَدۡرُسُونَ
Ko kuna da wani littafi, wanda a cikinsa, kuke karantãwa?
Ibisobanuro by'icyarabu:
إِنَّ لَكُمۡ فِيهِ لَمَا تَخَيَّرُونَ
Cẽwã kunã da, a cikinsa lalle (duk) abin da rãyukanku suka zãɓa?
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَمۡ لَكُمۡ أَيۡمَٰنٌ عَلَيۡنَا بَٰلِغَةٌ إِلَىٰ يَوۡمِ ٱلۡقِيَٰمَةِ إِنَّ لَكُمۡ لَمَا تَحۡكُمُونَ
Kõ kunã (riƙe) da wasu rantsuwõyin alkawari a kan Mu, har ya zuwa Rãnar ¡iyãma, cẽwa lalle ne kunã da abin da kuke hukuntã wa kanku?
Ibisobanuro by'icyarabu:
سَلۡهُمۡ أَيُّهُم بِذَٰلِكَ زَعِيمٌ
Ka tambaye su, wãne, a cikinsu, ke lãmuncewã ga sãmun wannan (hukuncin)?
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَمۡ لَهُمۡ شُرَكَآءُ فَلۡيَأۡتُواْ بِشُرَكَآئِهِمۡ إِن كَانُواْ صَٰدِقِينَ
Kõ sunã da abõkan tãrẽwa (ga wannan ra'ayi)? To, sai su kãwo abõkan tãrayyarsu, idan sun kasance mãsu gaskiya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
يَوۡمَ يُكۡشَفُ عَن سَاقٖ وَيُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ فَلَا يَسۡتَطِيعُونَ
Ranar da zã a kuranye ƙwabri, kuma a kira su zuwa ga yin sujada, sai bã zã su iyãwa ba.
Ibisobanuro by'icyarabu:
خَٰشِعَةً أَبۡصَٰرُهُمۡ تَرۡهَقُهُمۡ ذِلَّةٞۖ وَقَدۡ كَانُواْ يُدۡعَوۡنَ إِلَى ٱلسُّجُودِ وَهُمۡ سَٰلِمُونَ
Su fito da idãnu ƙasƙantattu, wulãkanci yana rufe su. Lalle ne a dã sun kasance anã kiran su zuwa, yin sujũdar, alhãli kuwa sunã lãfiya lau, (suka ƙi yi).
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَذَرۡنِي وَمَن يُكَذِّبُ بِهَٰذَا ٱلۡحَدِيثِۖ سَنَسۡتَدۡرِجُهُم مِّنۡ حَيۡثُ لَا يَعۡلَمُونَ
Sabõda haka ka bar Ni da mai ƙaryata wanna lãbãri (Alƙur'ãni). Zã Mu yi musu istidrãji daga inda ba su sani ba.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَأُمۡلِي لَهُمۡۚ إِنَّ كَيۡدِي مَتِينٌ
Ina jinkirtã musu, lalle kaidi Na mai ƙarfi ne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَمۡ تَسۡـَٔلُهُمۡ أَجۡرٗا فَهُم مِّن مَّغۡرَمٖ مُّثۡقَلُونَ
Kõ kana tambayar su wata la'ada ne, sabõda haka sũ, daga wannan tãrar, suke jin an nauyaya musu?
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَمۡ عِندَهُمُ ٱلۡغَيۡبُ فَهُمۡ يَكۡتُبُونَ
Ko kuma sunã da ilmin gaibu ne, wãto sunã yin rubũtun (abin da suke faɗã daga gare shi) ne?
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱصۡبِرۡ لِحُكۡمِ رَبِّكَ وَلَا تَكُن كَصَاحِبِ ٱلۡحُوتِ إِذۡ نَادَىٰ وَهُوَ مَكۡظُومٞ
Sabõda haka, ka yi haƙuri da hukuncin Ubangijinka, kada ka zama kamar Ma'abũcin kĩfi, alõkacin da ya yi kira, alhãli yana cike da hushi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
لَّوۡلَآ أَن تَدَٰرَكَهُۥ نِعۡمَةٞ مِّن رَّبِّهِۦ لَنُبِذَ بِٱلۡعَرَآءِ وَهُوَ مَذۡمُومٞ
Ba dõmin ni'ima daga wajen Ubangijinsa tã riske shi ba, lalle ne da an jẽfa shi a cikin wõfintacciyar ƙasa, alhãli yanã abin zargi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَٱجۡتَبَٰهُ رَبُّهُۥ فَجَعَلَهُۥ مِنَ ٱلصَّٰلِحِينَ
Sai Ubangijinsa Ya zãɓe shi, sa'an nan Ya sanya shi a cikin mutãnen kirki.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَإِن يَكَادُ ٱلَّذِينَ كَفَرُواْ لَيُزۡلِقُونَكَ بِأَبۡصَٰرِهِمۡ لَمَّا سَمِعُواْ ٱلذِّكۡرَ وَيَقُولُونَ إِنَّهُۥ لَمَجۡنُونٞ
Kuma lalle, ne waɗanda suka kãfirta sunã yin kamar su kãyar da kai sabõ da kallonsu (kallon mãmãki), a lokacin da suke jin karãtun Alƙur'ãni, kuma sunã cẽwa, "Lalle ne shi mahaukaci ne!"
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَمَا هُوَ إِلَّا ذِكۡرٞ لِّلۡعَٰلَمِينَ
Shi (Alƙur'ãni) bai kasance ba, fãce abin tunãtarwa ne ga duka dũniya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
 
Ibisobanuro by'amagambo Isura: Alqalam (Ikaramu)
Urutonde rw'amasura numero y'urupapuro
 
Ibisobanuro bya qoran ntagatifu - Ibisobanuro mu gihawusawiya - abubakar djumiy - Ishakiro ry'ibisobanuro

ibisobanuro bya Qoraan ntagatifu mururimi rw'igihawusa byasobanuwe na Abuubakri Muhamudi Juumi byakosowe kd bihagararirwa nikigo rawaad tarjamat hagamijwe kugera kubisonuro byumwimerere no kungurana ibitekerezo niterambere rirambye

Gufunga