Salin ng mga Kahulugan ng Marangal na Qur'an - Salin sa Wikang Hausa ni Abubakr Gumi * - Indise ng mga Salin

XML CSV Excel API
Please review the Terms and Policies

Salin ng mga Kahulugan Surah: Adh-Dhāriyāt   Ayah:

Suratu Al'thariyat

وَٱلذَّٰرِيَٰتِ ذَرۡوٗا
Inã rantsuwa da iskõki mãsu shẽkar abũbuwa, shẽƙẽwa.
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَٱلۡحَٰمِلَٰتِ وِقۡرٗا
Sa'an nan da girãgizai mãsu ɗaukar nauyi (na ruwa).
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَٱلۡجَٰرِيَٰتِ يُسۡرٗا
Sa'an nan da jirãge mãsu gudãna (a kan ruwa) da sauƙi.
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَٱلۡمُقَسِّمَٰتِ أَمۡرًا
Sa'an nan da Malã'iku mãsu rabon al'amari (bisa umurnin Allah).
Ang mga Tafsir na Arabe:
إِنَّمَا تُوعَدُونَ لَصَادِقٞ
Lalle abin da ake yi muku alkawari (da zuwansa), haƙĩƙa gaskiya ne.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَإِنَّ ٱلدِّينَ لَوَٰقِعٞ
Kuma lalle sakamako (ga ayyukanku), haƙĩƙa, mai aukuwa ne
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَٱلسَّمَآءِ ذَاتِ ٱلۡحُبُكِ
Inã rantsuwa da samã ma'abũciyar hanyõyi (na tafiyar taurãri da sautin rediyo).
Ang mga Tafsir na Arabe:
إِنَّكُمۡ لَفِي قَوۡلٖ مُّخۡتَلِفٖ
Lalle kũ, haƙĩƙa, kunã cikin magana mai sãɓa wa juna (game da Alƙur'ani).
Ang mga Tafsir na Arabe:
يُؤۡفَكُ عَنۡهُ مَنۡ أُفِكَ
Anã karkatar da wanda aka jũyar (daga gaskiya).
Ang mga Tafsir na Arabe:
قُتِلَ ٱلۡخَرَّٰصُونَ
An la'ani mãsu ƙiri-faɗi.
Ang mga Tafsir na Arabe:
ٱلَّذِينَ هُمۡ فِي غَمۡرَةٖ سَاهُونَ
Waɗanda suke shagala a cikin zurfin jãhilci.
Ang mga Tafsir na Arabe:
يَسۡـَٔلُونَ أَيَّانَ يَوۡمُ ٱلدِّينِ
Sunã tambaya: "Yaushe ne rãnar sakamako zã ta auku?"
Ang mga Tafsir na Arabe:
يَوۡمَ هُمۡ عَلَى ٱلنَّارِ يُفۡتَنُونَ
Ranar da suke a kan wuta anã fitinar su.
Ang mga Tafsir na Arabe:
ذُوقُواْ فِتۡنَتَكُمۡ هَٰذَا ٱلَّذِي كُنتُم بِهِۦ تَسۡتَعۡجِلُونَ
(A ce musu): "Ku ɗanɗani fitinarku, wannan shĩ ne abin da kuka kasance kunã nẽman zuwansa da gaggãwa."
Ang mga Tafsir na Arabe:
إِنَّ ٱلۡمُتَّقِينَ فِي جَنَّٰتٖ وَعُيُونٍ
Lalle mãsu taƙawa, sunã a cikin lambunan itãce da marẽmari.
Ang mga Tafsir na Arabe:
ءَاخِذِينَ مَآ ءَاتَىٰهُمۡ رَبُّهُمۡۚ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَبۡلَ ذَٰلِكَ مُحۡسِنِينَ
Sunã mãsu dĩbar abin da Ubangijinsu Ya bã su. Lalle sũ, sun kasance mãsu kyautatãwa a gabãnin haka (a dũniya).
Ang mga Tafsir na Arabe:
كَانُواْ قَلِيلٗا مِّنَ ٱلَّيۡلِ مَا يَهۡجَعُونَ
Sun kasance a lõkaci kaɗan na dare suke yin barci.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَبِٱلۡأَسۡحَارِ هُمۡ يَسۡتَغۡفِرُونَ
Kuma a lõkutan asuba sunã ta yin istigfãri.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَفِيٓ أَمۡوَٰلِهِمۡ حَقّٞ لِّلسَّآئِلِ وَٱلۡمَحۡرُومِ
Kuma a cikin dũkiyarsu akwai hakki ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hana wa rõƙo.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَفِي ٱلۡأَرۡضِ ءَايَٰتٞ لِّلۡمُوقِنِينَ
Kuma a cikin ƙasã akwai ãyõyi ga mãsu yaƙĩni.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَفِيٓ أَنفُسِكُمۡۚ أَفَلَا تُبۡصِرُونَ
Kuma a cikin rãyukanku (akwai ãyõyi). To, bã zã ku dũbã ba?
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَفِي ٱلسَّمَآءِ رِزۡقُكُمۡ وَمَا تُوعَدُونَ
Kuma a cikin sama arzikinku (yake fitõwa) da abin da ake yi muku alkawari.
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَوَرَبِّ ٱلسَّمَآءِ وَٱلۡأَرۡضِ إِنَّهُۥ لَحَقّٞ مِّثۡلَ مَآ أَنَّكُمۡ تَنطِقُونَ
To, kuma Ina rantsuwa da Ubangijin sama da ƙasã, lalle shĩ (abin da ake yi muku alkawari), haƙĩƙa gaskiya ne, kamar abin da kuka zamo kunã karantãwa na magana,
Ang mga Tafsir na Arabe:
هَلۡ أَتَىٰكَ حَدِيثُ ضَيۡفِ إِبۡرَٰهِيمَ ٱلۡمُكۡرَمِينَ
Shin, lãbãrin Bãƙin Ibrãhĩm, waɗanda aka girmama, ya zo maka?
Ang mga Tafsir na Arabe:
إِذۡ دَخَلُواْ عَلَيۡهِ فَقَالُواْ سَلَٰمٗاۖ قَالَ سَلَٰمٞ قَوۡمٞ مُّنكَرُونَ
A lõkacin da suka shiga gare shi, sai suka yi sallama; ya ce "Aminci ya tabbata a gare ku, mutãne bãƙi!"
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَرَاغَ إِلَىٰٓ أَهۡلِهِۦ فَجَآءَ بِعِجۡلٖ سَمِينٖ
Sai ya jũya zuwa ga iyãlinsa, sa'an nan ya zo da maraƙi tutturna,
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَقَرَّبَهُۥٓ إِلَيۡهِمۡ قَالَ أَلَا تَأۡكُلُونَ
Sai ya kusantar da shi zuwa gare su, ya ce: "Bã zã ku ci ba?"
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَأَوۡجَسَ مِنۡهُمۡ خِيفَةٗۖ قَالُواْ لَا تَخَفۡۖ وَبَشَّرُوهُ بِغُلَٰمٍ عَلِيمٖ
Sai ya ji tsõro daga gare su. Suka ce: "Kada kaji tsõro." Kuma suka yi masa bushãra da (haihuwar) wani yaro mai ilmi.
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَأَقۡبَلَتِ ٱمۡرَأَتُهُۥ فِي صَرَّةٖ فَصَكَّتۡ وَجۡهَهَا وَقَالَتۡ عَجُوزٌ عَقِيمٞ
Sai matarsa ta fuskanta cikin ƙyallõwa, har ta mari fuskarta kuma ta ce: "Tsõhuwa bakarãriya (zã ta haihu)!"
Ang mga Tafsir na Arabe:
قَالُواْ كَذَٰلِكِ قَالَ رَبُّكِۖ إِنَّهُۥ هُوَ ٱلۡحَكِيمُ ٱلۡعَلِيمُ
Suka ce: "Kamar haka Ubangijinki Ya faɗa. Lalle Shĩ, Shĩ ne Mai hikima, Mai ilmi."
Ang mga Tafsir na Arabe:
۞ قَالَ فَمَا خَطۡبُكُمۡ أَيُّهَا ٱلۡمُرۡسَلُونَ
(Ibrãĩm) ya ce: "To mẽne ne babban al'almarinku, yã kũ Manzanni!"
Ang mga Tafsir na Arabe:
قَالُوٓاْ إِنَّآ أُرۡسِلۡنَآ إِلَىٰ قَوۡمٖ مُّجۡرِمِينَ
Suka ce: "Lalle mũ, an aike mu zuwa ga waɗansu mutãne, mãsu laifi.
Ang mga Tafsir na Arabe:
لِنُرۡسِلَ عَلَيۡهِمۡ حِجَارَةٗ مِّن طِينٖ
"Dõmin mu saka musu waɗansu duwãtsu na wani yumɓu (bom).
Ang mga Tafsir na Arabe:
مُّسَوَّمَةً عِندَ رَبِّكَ لِلۡمُسۡرِفِينَ
"Waɗanda aka yi wa alãma daga wajen Ubangijinka, dõmin mãsu ɓarna."
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَأَخۡرَجۡنَا مَن كَانَ فِيهَا مِنَ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Sa'an, nan Muka fitar da wanda ya kasance a cikinta daga mũminai.
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَمَا وَجَدۡنَا فِيهَا غَيۡرَ بَيۡتٖ مِّنَ ٱلۡمُسۡلِمِينَ
Sai dai ba mu sãmu ba, a cikinta, fãce gida guda na Musulmi.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَتَرَكۡنَا فِيهَآ ءَايَةٗ لِّلَّذِينَ يَخَافُونَ ٱلۡعَذَابَ ٱلۡأَلِيمَ
Kuma Muka bar wata ãyã, a cikinta, ga waɗanda ke jin tsõron azãba, mai raɗaɗi.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَفِي مُوسَىٰٓ إِذۡ أَرۡسَلۡنَٰهُ إِلَىٰ فِرۡعَوۡنَ بِسُلۡطَٰنٖ مُّبِينٖ
Kuma ga Mũsã, a lõkacin da Muka aiko shi zuwa ga Fir'auna da wani dalĩli bayyananne.
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَتَوَلَّىٰ بِرُكۡنِهِۦ وَقَالَ سَٰحِرٌ أَوۡ مَجۡنُونٞ
Sai ya jũya bãya tãre da ƙarfinsa, kuma ya ce: "Mai sihiri ne kõ kuwa mahaukaci!"
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَأَخَذۡنَٰهُ وَجُنُودَهُۥ فَنَبَذۡنَٰهُمۡ فِي ٱلۡيَمِّ وَهُوَ مُلِيمٞ
Sabõda haka, Muka kama shi tãre da rundunarsa, sa'an nan Muka jẽfa su a cikin tẽku, alhãli kuwa yanã wanda ake zargi.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَفِي عَادٍ إِذۡ أَرۡسَلۡنَا عَلَيۡهِمُ ٱلرِّيحَ ٱلۡعَقِيمَ
Kuma ga Ãdãwa, a lõkacin da Muka aika iska ƙẽƙasasshiya a kansu.
Ang mga Tafsir na Arabe:
مَا تَذَرُ مِن شَيۡءٍ أَتَتۡ عَلَيۡهِ إِلَّا جَعَلَتۡهُ كَٱلرَّمِيمِ
Bã ta barin kõme da ta jẽ a kansa, fãce ta mayar da shi kamar rududdugaggun ƙasũsuwa.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَفِي ثَمُودَ إِذۡ قِيلَ لَهُمۡ تَمَتَّعُواْ حَتَّىٰ حِينٖ
Kuma ga Samũdãwa, a lõkacin da aka ce musu: "Ku ji ɗan dãɗi har wani ɗan lõkaci,"
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَعَتَوۡاْ عَنۡ أَمۡرِ رَبِّهِمۡ فَأَخَذَتۡهُمُ ٱلصَّٰعِقَةُ وَهُمۡ يَنظُرُونَ
Sai suka yi girman kai ga umurnin Ubangijinsu, sabõda haka tsãwa ta kãma su, alhãli kuwa sunã kallo.
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَمَا ٱسۡتَطَٰعُواْ مِن قِيَامٖ وَمَا كَانُواْ مُنتَصِرِينَ
Ba su kõ sãmu dãmar tsayãwa ba, kuma ba su kasance mãsu nẽman ãgaji ba.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَقَوۡمَ نُوحٖ مِّن قَبۡلُۖ إِنَّهُمۡ كَانُواْ قَوۡمٗا فَٰسِقِينَ
Da mutãnen Nũhu a gabãnin haka, lalle sun kasance waɗansu irin mutãne ne fãsiƙai.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَٱلسَّمَآءَ بَنَيۡنَٰهَا بِأَيۡيْدٖ وَإِنَّا لَمُوسِعُونَ
Kuma sama, mun gina ta da wani irin ƙarfi, alhãli kuwa lalle Mũ ne Mãsu yalwatãwa.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَٱلۡأَرۡضَ فَرَشۡنَٰهَا فَنِعۡمَ ٱلۡمَٰهِدُونَ
Kuma ƙasã Mun shimfiɗa ta, To, madalla da mãsu shimfiɗãwa, Mũ,
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَمِن كُلِّ شَيۡءٍ خَلَقۡنَا زَوۡجَيۡنِ لَعَلَّكُمۡ تَذَكَّرُونَ
Kuma daga kõme Mun halitta nau'i biyu, watakila zã ku yi tunãni.
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَفِرُّوٓاْ إِلَى ٱللَّهِۖ إِنِّي لَكُم مِّنۡهُ نَذِيرٞ مُّبِينٞ
Sabõda haka ku gudu zuwa ga Allah, lalle nĩ mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَلَا تَجۡعَلُواْ مَعَ ٱللَّهِ إِلَٰهًا ءَاخَرَۖ إِنِّي لَكُم مِّنۡهُ نَذِيرٞ مُّبِينٞ
Kuma kada ku sanya, tãre da Allah wani abin bautãwa na dabam, lalle nĩ, mai gargaɗi kawai ne a gare ku, mai bayyanannen gargaɗi.
Ang mga Tafsir na Arabe:
كَذَٰلِكَ مَآ أَتَى ٱلَّذِينَ مِن قَبۡلِهِم مِّن رَّسُولٍ إِلَّا قَالُواْ سَاحِرٌ أَوۡ مَجۡنُونٌ
Kamar haka dai wani Manzo bai jẽ wa waɗanda ke gabãninsu ba fãce sun ce: "Mai sihiri ne kõ mahaukaci."
Ang mga Tafsir na Arabe:
أَتَوَاصَوۡاْ بِهِۦۚ بَلۡ هُمۡ قَوۡمٞ طَاغُونَ
shin, sunã yi wa jũna wasiyya da shi ne? Ã'a, sũ dai mutãne ne mãsu girman kai.
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَتَوَلَّ عَنۡهُمۡ فَمَآ أَنتَ بِمَلُومٖ
Sai ka jũya daga barinsu, kuma kai ba abin zargi ba ne.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَذَكِّرۡ فَإِنَّ ٱلذِّكۡرَىٰ تَنفَعُ ٱلۡمُؤۡمِنِينَ
Kuma ka tunãtar, dõmin tunãtarwa tanã amfãnin mũminai.
Ang mga Tafsir na Arabe:
وَمَا خَلَقۡتُ ٱلۡجِنَّ وَٱلۡإِنسَ إِلَّا لِيَعۡبُدُونِ
Kuma Ban halitta aljannu da mutãne ba sai dõmin su bauta Mini.
Ang mga Tafsir na Arabe:
مَآ أُرِيدُ مِنۡهُم مِّن رِّزۡقٖ وَمَآ أُرِيدُ أَن يُطۡعِمُونِ
Bã Ni nufln (sãmun) wani arziki daga gare su, Bã Ni nufin su (yi Mini hidimar) ciyar da Ni.*
* Bã Ni nufin su sãmo Mini abinci, kuma bã Ni nufin su dafa Mini abinci.
Ang mga Tafsir na Arabe:
إِنَّ ٱللَّهَ هُوَ ٱلرَّزَّاقُ ذُو ٱلۡقُوَّةِ ٱلۡمَتِينُ
Lalle Allah, Shĩ ne Mai azurtãwa, Mai ĩkon yi, Mai cikakken ƙarfi.
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَإِنَّ لِلَّذِينَ ظَلَمُواْ ذَنُوبٗا مِّثۡلَ ذَنُوبِ أَصۡحَٰبِهِمۡ فَلَا يَسۡتَعۡجِلُونِ
To, lalle waɗanda suka yi zãlunci sunã da masaki (na ɗĩban zunubi) kamar masakin abõkansu, sabõda haka kada su yi Mini gaggãwa.
Ang mga Tafsir na Arabe:
فَوَيۡلٞ لِّلَّذِينَ كَفَرُواْ مِن يَوۡمِهِمُ ٱلَّذِي يُوعَدُونَ
Sabõda haka, bone ya tabbata ga waɗanda suka kãfirta, daga rãnar su wadda aka yi musu alkawari.
Ang mga Tafsir na Arabe:
 
Salin ng mga Kahulugan Surah: Adh-Dhāriyāt
Indise ng mga Surah Numero ng Pahina
 
Salin ng mga Kahulugan ng Marangal na Qur'an - Salin sa Wikang Hausa ni Abubakr Gumi - Indise ng mga Salin

Salin ng mga Kahulugan ng Marangal na Qur'an sa Wikang Hausa. Isinalin ito ni Abubakr Mahmoud Gumi. Inilathala ito ng King Fahd Glorious Quran Printing Complex sa Madinah Munawwarah, imprenta ng taong 1412 H. Isinagawa ang pagtatama nito sa pangangasiwa ng Sentro ng Rowad sa Pagsasalin. PInapayagan ang tumingin sa orihinal na salin sa layuning magpahayag ng pananaw, magsiyasat, at patuloy na paglinang.

Isara