Ibisobanuro bya qoran ntagatifu - Ibisobanuro mu gihawusawiya - abubakar djumiy * - Ishakiro ry'ibisobanuro

XML CSV Excel API
Please review the Terms and Policies

Ibisobanuro by'amagambo Isura: Abasa (Yazinze Umunya)   Umurongo:

Suratu Abasa

عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ
Yã game huska* kuma ya jũya bãya.
* Wani makãho, Abdullahi bin Ummi Maktũm ya je wurin Annabi dõmin ya musulunta, sai ya iske a lõkacin nan Annabi na ƙõƙarin shiryar da wasu manyan mutãne na Ƙuraishãwa, sai wannan makãhon ya yanke maganar Annabi da su, bã da saninsa ba, alhãli Annabi na bũrin su musulunta dõmin darajarsu ga idon mutãnensu. Saboda haka Annabi, (tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi), ya ɓata Fuska, ya tafi dõmin ɓacin ransa, saboda rashin musuluntarsu. Bãyan haka Annabi nã girmama Abdullahi ƙwarai, idan ya je wurinsa sai ya ce masa "Maraba da wanda Ubangijina Ya zarge ni sabõda shi." Kuma ya shimfiɗa masa mayafinsa, idan ya fita tafiya, yakan sanya shi riƙon garin Madina, ƙissar tana nũna girmamawar Allah ga Annabi da Ya ce: "Ya game Fuska." Bai ce masa: "Domin ka game Fuska" ba, sai ya faɗa a cikin hali mai sauƙi.".
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَن جَآءَهُ ٱلۡأَعۡمَىٰ
Sabõda makãho yã je masa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَمَا يُدۡرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ
To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَوۡ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكۡرَىٰٓ
Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَمَّا مَنِ ٱسۡتَغۡنَىٰ
Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأَنتَ لَهُۥ تَصَدَّىٰ
Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَمَا عَلَيۡكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ
To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَأَمَّا مَن جَآءَكَ يَسۡعَىٰ
Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَهُوَ يَخۡشَىٰ
Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأَنتَ عَنۡهُ تَلَهَّىٰ
Kai kuma kã shagala ga barinsa!
Ibisobanuro by'icyarabu:
كَلَّآ إِنَّهَا تَذۡكِرَةٞ
A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ
Sabõda wanda ya so ya tuna Shi (Allah).
Ibisobanuro by'icyarabu:
فِي صُحُفٖ مُّكَرَّمَةٖ
(Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,
Ibisobanuro by'icyarabu:
مَّرۡفُوعَةٖ مُّطَهَّرَةِۭ
Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
بِأَيۡدِي سَفَرَةٖ
A cikin hannãyen mala'iku marubũta.
Ibisobanuro by'icyarabu:
كِرَامِۭ بَرَرَةٖ
Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.
Ibisobanuro by'icyarabu:
قُتِلَ ٱلۡإِنسَٰنُ مَآ أَكۡفَرَهُۥ
An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!
Ibisobanuro by'icyarabu:
مِنۡ أَيِّ شَيۡءٍ خَلَقَهُۥ
Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?
Ibisobanuro by'icyarabu:
مِن نُّطۡفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ
Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).
Ibisobanuro by'icyarabu:
ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ
Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقۡبَرَهُۥ
Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.
Ibisobanuro by'icyarabu:
ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ
Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
كَلَّا لَمَّا يَقۡضِ مَآ أَمَرَهُۥ
Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَلۡيَنظُرِ ٱلۡإِنسَٰنُ إِلَىٰ طَعَامِهِۦٓ
To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أَنَّا صَبَبۡنَا ٱلۡمَآءَ صَبّٗا
Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
ثُمَّ شَقَقۡنَا ٱلۡأَرۡضَ شَقّٗا
Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَأَنۢبَتۡنَا فِيهَا حَبّٗا
Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَعِنَبٗا وَقَضۡبٗا
Da inabi da ciyãwa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَزَيۡتُونٗا وَنَخۡلٗا
Da zaitũni da itãcen dabĩno.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَحَدَآئِقَ غُلۡبٗا
Da lambuna, mãsu yawan itãce.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَفَٰكِهَةٗ وَأَبّٗا
Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
مَّتَٰعٗا لَّكُمۡ وَلِأَنۡعَٰمِكُمۡ
Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.
Ibisobanuro by'icyarabu:
فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ
To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.
Ibisobanuro by'icyarabu:
يَوۡمَ يَفِرُّ ٱلۡمَرۡءُ مِنۡ أَخِيهِ
Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ
Da uwarsa da ubansa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ
Da mãtarsa da ɗiyansa.
Ibisobanuro by'icyarabu:
لِكُلِّ ٱمۡرِيٕٖ مِّنۡهُمۡ يَوۡمَئِذٖ شَأۡنٞ يُغۡنِيهِ
Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وُجُوهٞ يَوۡمَئِذٖ مُّسۡفِرَةٞ
Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.
Ibisobanuro by'icyarabu:
ضَاحِكَةٞ مُّسۡتَبۡشِرَةٞ
Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.
Ibisobanuro by'icyarabu:
وَوُجُوهٞ يَوۡمَئِذٍ عَلَيۡهَا غَبَرَةٞ
Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.
Ibisobanuro by'icyarabu:
تَرۡهَقُهَا قَتَرَةٌ
Baƙi zai rufe su.
Ibisobanuro by'icyarabu:
أُوْلَٰٓئِكَ هُمُ ٱلۡكَفَرَةُ ٱلۡفَجَرَةُ
Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).
Ibisobanuro by'icyarabu:
 
Ibisobanuro by'amagambo Isura: Abasa (Yazinze Umunya)
Urutonde rw'amasura numero y'urupapuro
 
Ibisobanuro bya qoran ntagatifu - Ibisobanuro mu gihawusawiya - abubakar djumiy - Ishakiro ry'ibisobanuro

ibisobanuro bya Qoraan ntagatifu mururimi rw'igihawusa byasobanuwe na Abuubakri Muhamudi Juumi byakosowe kd bihagararirwa nikigo rawaad tarjamat hagamijwe kugera kubisonuro byumwimerere no kungurana ibitekerezo niterambere rirambye

Gufunga